Zauren Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya ya ƙaddamar da Kwamitin Amintattu na Asusun Tsaron Arewacin Najeriya a wani sabon yunƙuri na ƙarfafa matakan da ake ɗauka wajen magance matsalolin tsaro da suka dabaibaye yankin.
Ana sa ran kwamitin zai jagoranci tattara kuɗaɗe da sauran tallafi, ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro, tare da tallafa wa tsare-tsaren haɗin gwiwa na yanki domin inganta zaman lafiya, kwanciyar hankali da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a jihohi goma sha tara na Arewacin Najeriya.
Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana a jihar Gombe, Aliyu Bala Gerengi ya ruwaito cewa an ƙaddamar da kwamitin ne yayin taron Dandalin Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya da aka gudanar a Sir Kashim Ibrahim House da ke Kaduna.
Kuma kwamitin ya ƙunshi mambobi ashirin da ɗaya daga jihohi goma sha tara na Arewa, inda jihohin Bauchi da Kaduna suka samu wakilai biyu kowacce.
An zaɓi mambobin ne bisa gogewa da ƙwarewarsu, ciki har da tsofaffin manyan hafsoshin soji da na ‘yan sanda, ƙwararrun ma’aikatan gwamnati da gogaggun masu gudanarwa.
Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Alhaji Yayale Ahmed, ne aka naɗa a matsayin Shugaban Kwamitin, yayin da tsohon Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Janar Luther Martin Agwai mai ritaya, zai kasance Mataimakin Shugaban Kwamitin.
Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, AIG Sunday Babaji, shi ne ke wakiltar jihar Gombe a cikin kwamitin.
Da yake ƙaddamar da kwamitin, Shugaban Dandalin Gwamnonin Jihohin Arewacin Najeriya kuma Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya tuna cewa a tarurrukan da dandalin ya gudanar a ranar 2 ga Disamban 2025 a Kaduna da kuma ranar 30 ga Maris, 2026 a Abuja, gwamnonin sun cimma matsaya cewa tabarbarewar tsaro a Arewacin Najeriya na buƙatar matakin gaggawa, haɗin gwiwa da tsari mai inganci.
Gwamna Inuwa Yahaya ya ce duk da cewa Gwamnatin Tarayya ce ke da alhakin tabbatar da tsaron ƙasa, haɗin kan jihohin Arewa yana da muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa ƙoƙarin gwamnatin tarayya ta hanyar musayar bayanan sirri, haɗin gwiwar yanki da ƙarfafa juriyar al’ummomi.
Ya bayyana cewa an kafa Asusun Tsaron Arewacin Najeriya ne domin tara kuɗaɗe da sauran tallafi, inganta haɗin gwiwar hukumomin tsaro, ƙarfafa musayar bayanan sirri da kuma tallafa wa ayyukan jami’an tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Gwamnan ya ce ƙaddamar da Kwamitin Amintattu shi ne babban mataki na farko wajen aiwatar da kudirin dandalin na tunkarar matsalar tsaro cikin tsari, haɗin kai, gaskiya da ɗorewa.
Ya buƙaci mambobin kwamitin su yi aiki tare da gwamnonin Arewa, hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki domin dawo da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba mai ɗorewa a yankin.
A nasa jawabin, Shugaban Kwamitin, Alhaji Yayale Ahmed, ya bayyana cewa matsalolin tsaron Arewacin Najeriya suna da sarkakiya, kuma suna buƙatar mafita mai ɗorewa ta hanyar haɗin kai da jajircewa.
Ya tabbatar wa gwamnonin cewa kwamitin zai gudanar da aikinsa cikin gaskiya, riƙon amana da ƙwarewa, tare da yin aiki kafada da kafada da duk masu ruwa da tsaki, ciki har da cibiyoyin gargajiya, domin cimma manufofin Asusun Tsaron.
Alhaji Yayale Ahmed ya kuma roƙi gwamnonin da su bai wa kwamitin cikakken ‘yancin gudanar da aikinsa ba tare da katsalandan ba, domin ya samu damar sauke nauyin da aka ɗora masa yadda ya kamata.


