Sanata Danjuma Goje ya sa kafa ya shure sasancin da ya ci tikitin takararsa ta Sanatan Gombe a APC
Sanatan da ke wakiltar yankin Gombe ta Tsakiya, Muhammad Danjuma Goje, ya yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta hanyar “consensus” da jam’iyyar APC a jihar Gombe ta ɗauka.
Idan Baku mance ba mun Kawo Muku cewa, shugabannin jam’iyyar sun amince da DCP Mohammed Ahmadu Deba (mai ritaya) a matsayin ɗan takarar APC na kujera da Goje ke riƙe da ita, a wani taro da aka gudanar ranar Lahadi ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.
Sai dai a wata sanarwa da hadiminsa kan harkokin shari’a, Barrista Saidu Mu’azu Kumo, ya fitar, Sanata Goje wanda ke neman wa’adi na biyar a Majalisar Dattawa ya ce taron “consensus” ɗin bai haɗa da dukkan ‘yan takarar da aka tantance ba, domin ya shafi Gwamna Yahaya ne kawai tare da wasu kaɗan daga cikin masu neman takarar.


