Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika

An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau
Published: December 12, 2025 at 8:05 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 12, 2025

Daruruwan mutane sun yi macin yau jumma’a a titunan babban birnin Guinea-Bissau, domin nuna rashin jin dadinsu da juyin mulkin da aka yi a watan da ya shige, tare da neman a sako shugabannin hamayya da aka kama aka tsare.

Masu zanga zanga sun yi arangama da dakarun tsaro a Bissau a yayin da suka toshe hanyoyi ta hanyar kona tayu da kuma yin kiran da a sako Domingos Pereira, shugaban jam’iyyar hamayya wanda aka kama a lokacin juyin mulkin.

Hafsoshin soja sun hambarar da shugaba Umaero Sissoco Embalo a ranar 26 ga watan nuwamba, kwana daya kafin hukumar zabe ta kasar ta bayyana sakamakon zaben shugaban kasar da aka yi.

Sojojin sun nada manjo janar Horta Inta-a a matsayin shugaban kasar na wucin gadi.

A yayin da wannan ke faruwa ne kuma shugabannin kungiyar tarayyar tattalin arzikin kasashen yankin na Afirka ta yamma, ECOWAS, suke shirin ganawa a Abuja, babban birnin tarayyar Naeriya domin tattauna lamarin na kasar Ginea-Bissau, tare da nazarin kafa mata takunkumi.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026
Next Post: Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi

Karin Labarai Masu Alaka

An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci Afrika
Gombe Ta Ƙaddamar da Allurar Rigakafin HIV Ta LEN PrEP Afrika
Majalisun Najeriya Sun Amince Ta Karin Kasafin Kudi Afrika
Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NUJ: Akwai Bukatar Samar Da Inshorar Lafiya Ga ‘Yan Jarida A Najeriya Rediyo
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
  • Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni
  • Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai
  • Gwamnatin Kano Zata Dauki Mataki Game Da Kisan Dorayi Tsaro
  • Rasha Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Harin Iran Afrika
  • Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
  • Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.