Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine
Published: December 23, 2025 at 8:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hare-haren makamai masu linzami da jiragen drone da Rasha ta kai yau talata sun kashe mutane akalla uku cikinsu har da karamin yaro daya a Ukraine, tare da haddasa daukewar wutar lantarki a sassa da dama.

Wadannan hare-haren dake zuwa a bayan wani sabon zagaye na tattaunawar neman kawo karshen yakin na shekaru 4, sun fi lahani ga cibiyoyin samar da wutar lantarki na yammacin kasar.

Kasar Poland wadda ke makwabtaka da Ukraine a yamma, sai da ta tayar da jiragen saman yakinta a saboda hare-haren sun wakana dab da bakin iyakarta.

Shugaba Volodymyr Zelensky yace Rasha ta kai hare hare a kan yankuna akalla 13 na kasar.

Rasha ta ce ta kai hari a kan cibiyoyin samar da makamashi da na soji na Ukraine, ta kuma kama wasu kananan garuruwa biyu a bakin daga, amma ba a ji ta bakin kasar Ukraine kan wannan ba, kuma an san a baya tana musanta duk wani ikirarin Rasha na samun galaba a bakin daga.

Ita ma Ukraine ta kai nata harin cikin daren a kan wata masana’anta a yankin Stavropol na kudancin Rasha, ta haddasa tashin wuta a wurin a cewar gwamnan wannan yanki, Vladimir Vladimirov.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Shugaban Amurka Donald Trump Yace Bai Taba Shiga Jirgin Jeffrey Epstein Ba
Next Post: Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
Kasar Congo Ta Dau Alwashin Bin Tsari Wajen Rarraba Ma’adanai Afrika
Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya Afrika
Iran Tace Jakadan Kasar Ta A Lebanon Zai Cigaba Da Zama A Beirut Afrika
Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Kasar Namibiya Tayi Watsi Da Yarjejeniya Tsakanin Ta Da Kamfanin Total Labarai
  • Kasar Amurka Ta Sayi Kamfanin Sada Zumunci Na Tik-Tok Amurka
  • Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika
  • An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran Afrika
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.