Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano
Published: January 10, 2026 at 5:33 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Akalla mutane 10 ne suka mutu, wasu da dama kuma sun jikkata a wani mummunan hadarin mota da ya afku a kan hanyar Jama’are zuwa Azare a kan titin Kano zuwa Maiduguri, inda wata motar haya ke dauke da fasinjoji daga Gombe zuwa Kano.

Hadarin ya faru ne, inda wata mota mai lambar rajista KTG 181 ZZ da ke dauke da fasinjoji 19 ta afka cikin hadari.

Hukumar Kiyaye Hadurra ta Kasa (FRSC) reshen jihar Bauchi ta tabbatar da faruwar lamarin.

Kwamandan Sector, CC Apaji Danladi Boyi, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai.

A cewar sa, binciken farko ya nuna cewa gudu fiye da kima, gajiya da kuma rashin iya sarrafa mota na iya haifar da hadarin, duk da cewa bincike na ci gaba da gudana.

Jami’an FRSC sun kai dauki cikin gaggawa, inda suka ceto wadanda suka jikkata kuma suka garzaya da su zuwa Asibitin Koyarwa na Tarayya, dake Azare, domin kula da lafiyarsu.

An ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a dakin ajiye gawa na asibitin, inda ake jiran ‘yan uwansu su zo su gane su.

Kwamanda Boyi ya kara da cewa Aikin Operation Zero na ci gaba da gudana a fadin jihar, kuma jami’an hukumar na sintiri sosai a manyan tituna.

Labarai

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu
Next Post: An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Game Da Matsalar Tsaro A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka Amurka
Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique Afrika
Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato Bidiyo
Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe Afrika
  • Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
  • Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025: Wasanni
  • Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
  • Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.