Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu
Published: January 9, 2026 at 7:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta sanar da kama mutane hudu tare da kwato dabbobi masu yawa da ake zargin an sace su, a wani yunkuri na dakile satar dabbobi da fashin shanu a fadin jihar.

A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, samamen ya gudana ne da hadin gwiwar ’yan sa-kai da mafarauta.

A yayin ayyukan, an kama wasu matasa a yankunan Yamaltu-Deba, Kaltungo da Balanga, tare da kwato shanu biyu, tumaki 274, awaki 54 da jaki guda.

Rundunar ta ce an gano wasu daga cikin dabbobin nan take daga hannun masu su, yayin da ake ci gaba da bincike domin gano sauran masu dabbobin da kuma cafke wadanda ke tsere.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya yaba da hadin gwiwar al’umma, tare da jaddada kudirin rundunar na yakar satar dabbobi da sauran laifuka. Ya kuma bukaci jama’a da su rika bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro.

’Yan sanda sun tabbatar da cewa za a gurfanar da dukkan wadanda aka kama gaban kotu bayan kammala bincike.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari
Next Post: Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
Wani Abu Ya Fashe A Asibitin Bagudo Dake Jihar Kebbi Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mawakiyar Amurka Cardi B. Ta Cashe A Saudi Araibiya Nishadi
  • Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar Labarai
  • Addini Ko Kabilanci Basu Da Gurbi Cikin Ta’addanci Labarai
  • Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
  • Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya Labarai
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.