Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu
Published: January 9, 2026 at 7:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta sanar da kama mutane hudu tare da kwato dabbobi masu yawa da ake zargin an sace su, a wani yunkuri na dakile satar dabbobi da fashin shanu a fadin jihar.

A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, samamen ya gudana ne da hadin gwiwar ’yan sa-kai da mafarauta.

A yayin ayyukan, an kama wasu matasa a yankunan Yamaltu-Deba, Kaltungo da Balanga, tare da kwato shanu biyu, tumaki 274, awaki 54 da jaki guda.

Rundunar ta ce an gano wasu daga cikin dabbobin nan take daga hannun masu su, yayin da ake ci gaba da bincike domin gano sauran masu dabbobin da kuma cafke wadanda ke tsere.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya yaba da hadin gwiwar al’umma, tare da jaddada kudirin rundunar na yakar satar dabbobi da sauran laifuka. Ya kuma bukaci jama’a da su rika bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro.

’Yan sanda sun tabbatar da cewa za a gurfanar da dukkan wadanda aka kama gaban kotu bayan kammala bincike.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari
Next Post: Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano

Karin Labarai Masu Alaka

An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
Matsayar Iran Na Kera Makamin Nuclear Bazai Sanja Ba Afrika
An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa Afrika
Shugaba Trump Ya Jinjinawa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya Afrika
Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Ta Tasa Keyar Wani Jirgi Shake Da Mai Sauran Duniya
  • Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
  • Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
  • Kasar China Ta Daina Bada Bashi Da Dalar Amurka Sai Da Kudin Kasar Yuan Labarai
  • Barayin Waya Sun Yanke Yatsun Hannu Guda Biyu Da Gefen Kunne A Bauchi Labarai
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare Tsaro
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.