Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi
Published: December 20, 2025 at 10:06 AM | By: Bala Hassan

Shugaba Tinubu ya buƙaci gwamnoni su mutunta hukuncin Kotun Ƙoli kan ’yancin kuɗin ƙananan hukumomi

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa na tabbatar da aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli da ya bai wa ƙananan hukumomi ’yancin karɓar kuɗaɗensu kai tsaye, ba tare da tsakura ba.

Shugaban Ƙasar ya bayyana hakan ne a daren Juma’a yayin taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) karo na 15 na jam’iyyar APC, wanda aka gudanar a Cibiyar Taron Fadar Gwamnati da ke Abuja.

Tinubu ya gargaɗi gwamnonin jihohi da su bi umarnin Kotun Ƙoli, yana mai cewa rashin yin hakan na iya tilasta masa ɗaukar wasu matakan zartarwa. Ya ce, Kotun Ƙolin ta yi umarni a bai wa ƙananan hukumomi kuɗaɗensu kai tsaye, kuma gwamnatinsa na sa ido kan yadda ake aiwatar da wannan hukunci.

Shugaban Ƙasar ya kuma buƙaci shugabannin APC su ƙarfafa haɗin kai a cikin jam’iyyar, yana mai tuna musu cewa jam’iyyar ta ginu ne kan siyasar ci gaba, haɗa kowa da kowa, da mutunta bambancin ra’ayi. A cewarsa, dole ne a kasance masu haƙuri da juna domin dimokuraɗiyyar Najeriya ta dore.

Dangane da tsaro, Tinubu ya ce kafa ’yan sandan jihohi shi ne mafita, inda ya buƙaci Majalisar Dokoki ta Ƙasa da ta gayyaci Sufeto Janar na ’Yan Sanda domin duba hanyoyin samar da tsari da kariya daga cin zarafi. Ya ce hakan na da muhimmanci wajen yaƙi da ta’addanci da ’yan bindiga.

Shugaban Ƙasar ya kuma nuna goyon bayansa ga ƙoƙarin ƙara yawan mata a muƙaman zaɓe, tare da shawartar Majalisar Tarayya da ta guji ƙoƙarin mayar da harkar caca (lottery) ƙarƙashin ikon tarayya, yana mai cewa al’amarin ya rataya ne a hannun jihohi.

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya yabawa Tinubu bisa jajircewarsa da kwarewarsa ta siyasa, yana mai cewa duk wata haɗaka da za ta nemi kalubalantar Tinubu a zaɓen 2027 ba za ta yi nasara ba. Ya ce Tinubu ya taka muhimmiyar rawa wajen gina adawar siyasa a Najeriya tun kafin hawansa mulki.

Shi ma Shugaban APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya sanar da fara shirin rajistar mambobin jam’iyyar ta hanyar na’ura (e-registration) a dukkanin matakai, tare da roƙon shugabanni da masu ruwa da tsaki su ba da haɗin kai. Ya kuma sanar da tsawaita wa’adin kwamitocin jam’iyyar na matakai daban-daban har zuwa Maris 2026.

A ƙarshe, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio da Gwamna Hope Uzodimma sun yaba wa Shugaban Ƙasar bisa tsare-tsaren gyaran tattalin arziƙi da suka ce na nufin bunƙasa tattalin arzikin ƙasa da walwalar al’umma.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki
Next Post: Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa

Karin Labarai Masu Alaka

Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci Afrika
Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Bincike Ya Nuna Cewar Da Wuya Iran Ta Bude Mashigin Hormuz Afrika
  • Ƙarin Albashi Zai Fara Aiki Ga Sojojin Najeriya Daga Satumba Afrika
  • Cutar Kurkunu Ta Kusa Zamowa Tarihi A Duniya Amurka
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
  • Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya Labarai
  • Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.