Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi
Published: December 17, 2025 at 8:40 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata kotu a kasar Faransa ta yanke hukuncin daurin shekaru 30 a gidan kurkuku a kan tsohon madugun ‘yan tawayen Kwango ta Kinshasa, Roger Lumbala, wanda ta samu da laifuffukan cin zarafin bil Adama a lokacin yakin Kwango na biyu.

‘Yan rajin ganin an hukumta masu aikata irin wadannan laifuffuka a gadin duniya sun yaba da wannan hukunci a zaman babban ci gaba na hukumta masu hannu a wannan yakin da ya kashe miliyoyin mutane.

A lokacin da yake bayyana hukuncin, alkalin wannan kotu dake birnin Paris, Marc Sommerer, yace Lumbala ya aikata ko ya bada umurnin aikatawa, ko ya tallafa wajen aikata munanan laifuffuka da kashe-kashe da fyade, da gana azaba, da bautarwa da sata da wawusa ko lalata dukiyoyi.

Wadannan laifuffukan da aka tuhumi Lumbala da aikatawa suna da alaka da wani farmakin da wata kungiyarsa mai samun goyon bayan kasar uganda a lokacin, ta kai a shekarun 2002 da kuma 2003 a arewa maso gabashin Kwango.

Sun kai hare-haren ne a kan ‘yan kabilun Nande da Bambuti wadanda suka zarga da laifin goyon bayan wata kungiyar daban ta sojojin sa kai a yankin.

An gudanar da yakin Kwango na biyu daga shekarar 1998 zuwa 2003. Kasashe har guda 9 suka tsoma baki da hannu a wannan yaki, kuma an kashe mutane fiye da miliyan 5, cikinsu har da wadanda suka mutu a sanadin yunwa da kuma cututtuka.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16
Next Post: Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum

Karin Labarai Masu Alaka

Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika
Babban Bankin Najeriya Ya Rage Kudin Ruwa Da Kashi Daya Cikin Dari Labarai
Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
  • Muhawara Mai Zafi Tsakanin APC da ADC Shirye-Shirye
  • Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe Tsaro
  • Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.