Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna
Published: January 2, 2026 at 12:20 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 2, 2026

Rasha da Ukraine suna zargin juna da auna hare hare kan farar hula a ranar farko ta sabuwar shekara, inda Rasha tayi zargin Ukraine ta kai mummunar hari akan wai O’tel a yankin kudancin kasar data mamaye, yayin da hukumomi a Kyivi suke zargin Rasha ta auna hare hare kan tashoshin makamashin wutan lantarki.

Rahotannin nan suna zuwa ne a dai dai lokacin da aka zafafa yin shawarwari da zummar kawo karshen yakin na kusan shekaru hudu, ko wacce daga cikin kasashen biyu masu gaba da juna, tana zargin dayar da kokarin cewa ra’ayinta ne ya fi samun karbuwa da goyon bayan shugaban Amurka.

“A ranar sabuwar shekara, da-gangan Rasha ta auna Ukraine da hare hare da jiragen drones da basu da matuka cikin dare.”

Shugaba Volodymyr Zelensky ya rubuta a shafin sa dake dandalin Telegram, yana mai cewa a hare haren, Rasha ta auna tashoshin samar da wutan lantarki a yankunan kasar bakwai.

A nata bangaren Rasha ta zargi Ukraine cewa ta kashe akalla mutane 24 ciki har da jariri a wani hari data kai da jiragen drones kan wani O’tel da wurn cin abinci da shakatawa a yayinda mutane suke murnar shigar sabuwar shekara a yankin Ukraine na Kherson dake kudancin kasar.

Sai dai da take magana, rundunar mayakan Ukraine wacce ta sha sukar Rasha a kan kai hare hare kan farar hula, tace hare haren da take kaiwa duka tana auna su ne kan cibiyoyin soja da kuma tashoshin makamashi, amma bata ce komi ba kan zargin kai hari kan O’tel ba.

Shugaba Zelensky yace, harin na Rasha yayinda ake hutun sabuwar shekara, ya nuna cewa Ukraine ba zata iya jurewa jinkiri kan kayan tsaro ta sararin samaniya ba.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi
Next Post: Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu

Karin Labarai Masu Alaka

Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki Labarai
Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika
Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
Chadi Ta Sauyawa ‘Yan Gudun Hijira Matsuguni Afrika
Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
Malaman Tsangaya A Gombe Sun Goyi Bayan Inuwa Yahaya Da Jamilu Gwamna Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
  • Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
  • Gurbin Yaya Tongo: INEC Ta Tsayar Da 19 Ga Satumba Don Zaɓen Cike Gurbi Afrika
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela Amurka
  • An Maka Wasu Jami’an Immigration A Kotu Bisa Zargin Rashin Da’a A Birtaniya Labarai
  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.