Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta a Najeriya wato (INEC) ta tsayar da Asabar, 19 ga Satumba, 2026 a matsayin ranar da za a gudanar da zaɓen cike gurbin kujerar wakiltar Gombe/Kwami/Funakaye a Majalisar Wakilan Tarayya.
Za a gudanar da zaɓen ne domin cike gurbin da ya samu sakamakon rasuwar ɗan majalisar da ke wakiltar mazabar, Honarabul Yaya Bauchi Tongo, wanda ya rasu yana da shekaru 62 bayan fama da gajeruwar rashin lafiya.
INEC ta bayyana cewa za a gudanar da zaɓen ne bisa tanadin Sashe na 76(2) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, kamar yadda aka yi wa gyara, da kuma sauran tanade-tanaden dokar zaɓe.
A cikin jadawalin da hukumar ta fitar, za a wallafa Sanarwar Zaɓe a ranar Alhamis, 20 ga Agusta, 2026.
Hukumar ta kuma tsara cewa jam’iyyun siyasar da ke da niyyar tsayar da ’yan takara su gudanar da zaɓen fidda gwani tsakanin 21 zuwa 25 ga Agusta, 2026.
Bayan kammala zaɓen fidda gwani da sauran matakan tantance ‘yan takara, INEC za ta wallafa jerin sunayen ’yan takarar da aka amince da su a ranar 8 ga Satumba, 2026.
A cewar jadawalin, yakin neman zaɓe na hukuma zai fara ne a 9 ga Satumba, sannan ya ƙare a 17 ga Satumba, 2026, kwanaki biyu kafin ranar zaɓen.
Mazabar Gombe/Kwami/Funakaye ta ƙunshi Kananan Hukumomi uku, wato Gombe, Kwami da Funakaye. INEC ta ce za a gudanar da zaɓen a faɗin rumfunan zaɓe 903 da yankunan rajista 31 na mazabar.
Hukumar ta yi kira ga dukkan jam’iyyun siyasa da ’yan takararsu da su bi jadawalin da aka tsara tare da gudanar da dukkan harkokinsu cikin bin dokokin zaɓe.
INEC ta kuma tabbatar wa masu ruwa da tsaki a mazabar cewa tana da cikakken shiri na gudanar da zaɓe cikin ’yanci, adalci da gaskiya, tare da samar da dama iri ɗaya ga dukkan jam’iyyun siyasa da ’yan takara.
Hukumar ta kuma yi kira ga masu kada kuri’a da su fito su gudanar da haƙƙinsu na ɗan ƙasa cikin lumana da sanin ya kamata.
Zaɓen na ranar 19 ga Satumba, 2026 na daga cikin zaɓukan cike guraben kujerun majalisun dokokin da INEC ta tsara gudanarwa a wasu jihohin Najeriya.


