Gwamnatin jihar Gombe dake arewa maso Gabashin Najeriya ta sake jaddada aniyarta na tabbatar da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya ta hanyar ƙarfafa matakan kare hanyoyin kiwo da kuma dazukan kiwo domin rage rikice-rikicen da ke faruwa tsakanin bangarorin biyu.
Wannan na ƙunshe ne cikin ziyarar duba aiki da Ƙaramin Kwamitin Aiwatar da Rahoton White Paper kan Hanyoyin Kiwo ya kai garin Jauro Jibir da ke Kwami, gundumar Bojude, da kuma Filin Kiwo na Ƙasa da Ƙasa na Kwalale da ke yankin Daban Fulani a jihar Gombe
Da yake jawabi ga al’ummar yankunan, ɗaya daga cikin mambobin kwamitin, Ardo Chindo Abubakar, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta umarci jama’a, musamman manoma, da su guji noma a cikin hanyoyin kiwo da filayen kiwo da aka keɓe domin wannan manufa.
Ya ce filayen kiwo mallakin Gwamnatin jihar Gombe ne, kuma an ware su ne domin kiwon dabbobi, yana mai cewa kiyaye su zai taimaka wajen rage rikice-rikice tsakanin manoma da makiyaya tare da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.
A nasa jawabin, Hakimin Bojude, Alhaji Ibrahim Dan Buram, da Hakimin Daban Fulani, Alhaji Muhammad Seyo, sun buƙaci al’ummominsu da su mara wa manufofin gwamnatin jihar baya tare da bai wa Kwamitin Aiwatar da Rahoton White Paper cikakken haɗin kai domin cimma nasarar aikin da aka ɗora masa.
Hakiman sun kuma shawarci jama’a da su kasance masu bin doka da oda, su guji duk wani abu da ka iya kawo tashin hankali ko ɓata sunan al’ummominsu da addininsu.
A nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Kwami, wanda shugaban Sashen Noma na ƙaramar hukumar, Muhammad Ibrahim Bojude, ya wakilta, ya yi kira ga jama’a, musamman manoma da makiyaya, da su mutunta dokokin da suka shafi hanyoyin kiwo tare da ba kwamitin cikakken goyon baya da haɗin kai.
Ya ce haɗin kan gwamnati, sarakunan gargajiya, manoma da makiyaya zai taimaka matuƙa wajen samar da zaman lafiya da bunƙasa harkokin noma da kiwo a Jihar Gombe.



