Tsohon mai ba da shawara kan harkokin siyasa ga tsohon Shugaban Ƙasar Najeriya Goodluck Jonathan kuma jigo a jam’iyyar APC, Farfesa Rufa’i Ahmed Alkali, ya yi jimamin rasuwar tsohon Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), Reshen Babban Birnin Tarayya (FCT), Comrade Patrick Osertin Osambedwan.
Farfesa Alkali ya bayyana rasuwar Osambedwan a matsayin babban rashi ga harkar aikin jarida da ma ƙasar Najeriya baki ɗaya, yana mai cewa marigayin ya taka muhimmiyar rawa wajen yaɗa gaskiya, tabbatar da ɗaukar nauyi da kuma yi wa al’umma hidima.
A cikin wata sanarwa, Alkali ya ce ya samu labarin rasuwar marigayin cikin matuƙar kaduwa da alhini, yana mai bayyana shi a matsayin ƙwararren ɗan jarida kuma mutum mai amana wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen kare martabar aikin jarida.
Ya ce ya san marigayin kuma sun yi aiki tare tsawon shekaru, musamman ta hanyar hulɗarsu a fannonin aikin gwamnati da kafafen yaɗa labarai.
Alkali ya bayyana Osambedwan a matsayin aminin amana, ƙwararren masani kuma mutum mai ƙarfin hali, wanda jajircewarsa wajen kare ƙa’idojin aikin jarida ta sa ya samu mutunci a tsakanin ’yan jarida, jami’an gwamnati da sauran al’umma.
A cewarsa, marigayin na cikin ƙarni na ’yan jarida da suka ɗauki aikin jarida a matsayin kira mai tsarki na yaɗa gaskiya, wayar da kan jama’a, tabbatar da ɗaukar nauyin masu mulki da kuma taimakawa wajen ci gaban ƙasa.
Farfesa Alkali ya ce Osambedwan ya kasance mai zurfin fahimta kan al’amuran ƙasa, tare da sadaukar da kansa wajen inganta jin daɗin ’yan jarida da kuma amfani da hanyar tattaunawa wajen magance matsalolin da suka shafi ƙasa.
Ya ƙara da cewa a tsawon aikinsa, marigayin ya tsaya tsayin daka wajen kare ƙwarewa a aikin jarida, ’yancin kafafen yaɗa labarai da kuma aikin jarida mai ɗaukar nauyi.
A lokacin da yake Shugaban NUJ na FCT, Alkali ya ce Osambedwan ya taka muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa ƙungiyar da kuma kare muradun ’yan jarida da ma’aikatan kafafen yaɗa labarai a Abuja da sauran sassan ƙasar.
Bayan rasuwar tasa, Farfesa Alkali ya kuma nuna damuwa kan yadda ake samun ƙarin asarar rayukan ’yan jarida a Babban Birnin Tarayya da sauran sassan Najeriya.
Ya ce abin damuwa ne yadda aka ci gaba da rasa ƙwararrun ma’aikatan kafafen yaɗa labarai cikin ɗan gajeren lokaci, yana mai cewa kowace rasuwa na nufin an rasa wani mutum mai ɗauke da ilimi, ƙwarewa da gogewar da al’umma ke matuƙar buƙata.
Ya yi kira ga masu ruwa da tsaki a harkar kafafen yaɗa labarai da gwamnati da ƙungiyoyin ’yan jarida da su ƙara mayar da hankali kan jin daɗin ’yan jarida, kiwon lafiyarsu da kuma samar da ingantaccen yanayin aiki.
Alkali ya ce ’yan jarida na sadaukar da rayukansu wajen sanar da jama’a, ilmantar da su da kuma wayar da kan al’umma, don haka ya zama wajibi a tabbatar da cewa ana ba su kulawa da tallafin da ya dace.
Yayin da yake jimamin rasuwar Osambedwan, Farfesa Alkali ya ce ya kamata a riƙa tunawa da marigayin saboda rayuwarsa ta hidima, mutunci, ƙwarewa, ƙarfin hali da kuma kishin ɗan Adam.
Ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, shugabanci da mambobin NUJ FCT, ’yan jarida da sauran ma’aikatan kafafen yaɗa labarai, abokai da duk waɗanda rasuwar ta shafa.
Farfesa Rufa’i Ahmed Alkali ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta wa marigayi Patrick Osertin Osambedwan kura-kuransa, Ya jikansa da rahama, Ya ba shi Aljannatul Firdaus, sannan Ya bai wa iyalansa da abokansa ƙarfin hali da haƙurin jure wannan babban rashi.


