Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Tinubu Ya Taya Shettima Murnar Cika Shekaru 60, Ya Yabi Gudunmawarsa Ga Najeriya
Published: September 1, 2026 at 8:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya taya Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, murnar cika shekaru 60 da haihuwa, tare da yabawa irin gudunmawar da ya bayar wajen yi wa Jihar Borno da Najeriya hidima.

A cikin saƙon taya murnar da ya fitar ranar Talata, 1 ga Satumba, 2026, Shugaba Tinubu ya bayyana Shettima a matsayin amintaccen abokin aiki, ɗan kishin ƙasa kuma mutumin da rayuwarsa ta kasance mai cike da hidima, jajircewa da sadaukarwa.

Ya ce yana taya matar Mataimakin Shugaban Ƙasar, Nana, da ’ya’yansa, iyalansa da abokan siyasarsa murnar wannan muhimmin zagayowar ranar haihuwa.

Shugaba Tinubu ya bayyana cewa a lokacin da Shettima yake gwamnan Jihar Borno, da kuma yanzu da yake riƙe da matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa, ya nuna ƙarfin hali, ƙwazo, tausayi da jajircewa wajen inganta rayuwar al’umma.

Ya kuma yaba da tarihin Shettima a fannin banki, tare da bayyana shi a matsayin mutum mai kishin ci gaban ƙasa da haɗin kan Najeriya.

Tinubu ya ce amincin Shettima ga jam’iyyar All Progressives Congress (APC), da goyon bayan da yake bai wa gwamnatin tarayya, da kuma jajircewarsa wajen tabbatar da nasarar ajandar Renewed Hope sun cancanci yabo.

Shugaban Ƙasar ya ƙara da cewa a matsayinsa na Shugaban Majalisar Tattalin Arziƙi ta Ƙasa (National Economic Council), Shettima ya samar da jagoranci mai ma’ana wajen daidaita manufofin tattalin arziki da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi.

Ya ce mutunta kundin tsarin mulki da cibiyoyin dimokuraɗiyya, tare da amfani da tattaunawa da shawarwari wajen tafiyar da al’amura, sun taimaka wajen ƙarfafa shugabanci nagari.

Tinubu ya bayyana hikimar Shettima, amincinsa da kuma fahimtar nauyin da ke kansa a matsayin muhimman abubuwan da suka taimaka wa gwamnatin.

Shugaban ya kuma gode wa Mataimakin nasa bisa irin goyon baya da haɗin gwiwar da yake ci gaba da ba shi wajen aiwatar da manufofin gwamnatin Renewed Hope da cika alkawuran da aka yi wa ’yan Najeriya.

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa haɗin gwiwar da ke tsakaninsu zai ci gaba da samar da ci gaba mai ma’ana wajen gina Najeriya mai inganci.

A ƙarshe, Shugaba Tinubu, a madadin Gwamnatin Tarayya, ya sake taya Shettima murnar cika shekaru 60, tare da yi masa addu’ar Allah Ya ci gaba da jagorantar sa, Ya kare shi, Ya ƙara masa hikima da lafiya, Ya kuma ba shi tsawon rai domin ci gaba da yi wa Najeriya hidima.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Lawanti Ya Ƙara Wa Gombe Daraja A Fannin Aikin Jarida – NUJ
Next Post: Rasuwar Tsohon Shugaban NUJ FCT, Osambedwan, Babban Rashi Ne — Ferfesa Alkali

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika
Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
Tsohon Shugaban Kasa Obasanjo Ya Ziyarci IBB Siyasa

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai
  • Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
  • Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Wani Bincike Ya Nuna Cewar Da Wuya Iran Ta Bude Mashigin Hormuz Afrika
  • Za a Fara Kakar Gasar Firimiya Ta Najeriya, NPFL, 2026/27 Yau Juma’a, 28 Ga Watan Agusta Wasanni
  • Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.