Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen jihar Gombe dake arewa maso Gabashin Najeriya ta taya Dr. Kabiru Danladi Lawanti murnar naɗinsa a matsayin Editor-at-Large na Media Trust.

NUJ Gombe ta bayyana naɗin a matsayin abin alfahari da kuma karramawa ga Lawanti, tare da bayyana shi a matsayin ƙwararren ɗan jarida mai dogon tarihi wajen gudanar da aikin jarida cikin kwarewa da kishin ƙasa.
Ƙungiyar ta ce naɗin ya nuna irin ƙwarewa da gogewar da Lawanti ya samu a fannin kafafen yaɗa labarai, tare da fatan cewa zai yi amfani da sabon matsayinsa wajen ƙara bunƙasa aikin jarida da inganta harkokin yaɗa labarai a Najeriya.
NUJ Gombe ta kuma yi masa fatan samun nasara a sabon matsayinsa, tare da ƙarfafa gwiwarsa wajen ci gaba da bayar da gudunmawa ga ci gaban aikin jarida da al’umma.


