Rundunar ’yan sandan jihar Kano a Najeriya ta ce ta ɗauki tsauraran matakan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya yayin bikin Takutaha na shekarar 2026, wanda ake sa ran gudanarwa a yau Talata, 1 ga Satumba.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya yaba wa al’ummar Kano bisa yadda suka kasance suna gudanar da bikin cikin lumana, haɗin kai da bin doka a shekarun baya.
Bakori ya kuma gode wa sarakunan gargajiya, malaman addini, shugabannin al’umma da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki, bisa haɗin gwiwar da suke bai wa rundunar wajen tabbatar da zaman lafiya.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar, rundunar ta ce ta tanadi matakan tsaro na musamman da suka haɗa da ayyukan leƙen asiri, sintiri na sa’o’i 24, binciken ababen hawa da mutane, da tura jami’an tsaro na musamman zuwa wuraren da za a gudanar da bikin.
Rundunar ta ce za a kuma sanya jami’an tsaro a hanyoyin shiga da fita da kuma wuraren da ake ganin za su iya zama barazana ga tsaro.
Kwamishinan ’yan sandan ya gargadi ’yan daba da masu tada zaune tsaye da su nisanci wuraren bikin, yana mai cewa rundunar ba za ta lamunci tashin hankali ko duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiyar jama’a ba.
Ya ce duk wanda aka kama yana karya doka za a gurfanar da shi gaban kotu domin fuskantar hukunci kamar yadda doka ta tanada.
Rundunar ta kuma bukaci al’umma da su gudanar da bikin cikin lumana, su kasance masu bin doka, tare da gaggauta kai rahoton duk wani mutum ko abu da suke zargi ga ofishin ’yan sanda mafi kusa ko kuma ta layukan gaggawa na rundunar.
Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta yi kira ga al’ummar jihar da su ba da cikakken haɗin kai domin ganin an gudanar da bikin Takutaha cikin zaman lafiya, farin ciki da annashuwa.


