Rundunar ’yan sandan jihar Kogi a Najeriya ta sanar da ceto wasu ’yan bautar ƙasa wato NYSC 10, da aka yi garkuwa da su a jihar.

’Yan bautar ƙasar na cikin waɗanda wasu ’yan bindiga suka sace a ranar Laraba, 26 ga watan Agusta, a kan hanyar Aloma-Egane, da ke Ƙaramar Hukumar Ofu ta Jihar Kogi.
Rahotanni sun ce ’yan NYSC ɗin na kan hanyarsu ne daga sansanin horas da matasa da ke Ƙaramar Hukumar Kolokuma/Opokuma a kihar Bayelsa, zuwa Abuja, bayan kammala shirinsu na horaswa.
Rundunar ’yan sandan ta ce maharan sun fito daga cikin daji ne a kusa da mahadar Ogene Zaria da Onicha-Igo, inda suka tare wasu motocin bas guda biyu tare da yin garkuwa da wasu daga cikin fasinjojin.
Bayan samun kiran neman agaji, jami’an tsaro sun isa wurin inda suka gano motocin bas ɗin da aka bari a wurin, sannan suka fara aikin bincike da tsefe dazuzzukan da ke yankin domin gano waɗanda aka yi garkuwa da su.
Tun da farko, rundunar ta sanar da ceto mutane 11, ciki har da direbobin motocin bas ɗin guda biyu, inda ta ce mafi yawansu ’yan NYSC ne.
A wani sabon aikin ceto kuma, rundunar ta ce an ƙara ceto wasu ’yan bautar ƙasa 10 ta hanyar haɗin gwiwar jami’an ’yan sanda, sojoji da Hukumar DSS.
Rundunar ta bayyana aikin ceto a matsayin wanda aka gudanar cikin haɗin gwiwa tare da amfani da bayanan sirri, domin tabbatar da tsaron waɗanda aka yi garkuwa da su, da kuma tarwatsa ayyukan masu aikata laifin.
Rundunar ta ce aikin bincike da ceto sauran waɗanda ake zargin har yanzu suna hannun masu garkuwa da mutane yana ci gaba, tare da kokarin gano tare da cafke waɗanda suka aikata laifin.
Kwamishinan ’yan sandan Jihar Kogi ya yaba wa jami’an ’yan sanda, sojoji, DSS da sauran jami’an tsaro da suka shiga aikin, bisa jajircewa da ƙwarewar da suka nuna wajen ceto waɗanda aka yi garkuwa da su.
Ya kuma gode wa al’ummar yankunan da abin ya shafa bisa haɗin kai da kuma samar da bayanan sirri da ke taimakawa jami’an tsaro wajen gudanar da ayyukansu.
Rundunar ta ƙara kira ga jama’a da su kasance cikin taka-tsantsan, tare da kai rahoton duk wani mutum ko motsi da suke zargi ga jami’an tsaro mafi kusa, domin taimakawa wajen tabbatar da tsaro a yankin.


