Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Al’umma Su Kiyaye Doka Yayin Bikin Takutaha Afrika
  • RUWASSA Ta Hada Masu Ruwa Da Tsaki Domin Inganta Aiwatar Da Shirin NG-SURWASH Afrika
  • Rundunar ’Yan Sandan Bauchi Ta Kama Dattijo Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ’Yar Shekara 8 Afrika
  • Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam Afrika
  • Gwamna Inuwa Yahaya Ya Jaddada Haƙuri Da Fahimtar Juna A Siyasa Afrika

’Yan Sanda, Sojoji Da DSS Sun Ceto ‘Yan NYSC Da Aka Sace A Kogi
Published: September 1, 2026 at 8:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ’yan sandan jihar Kogi a Najeriya ta sanar da ceto wasu ’yan bautar ƙasa wato NYSC 10, da aka yi garkuwa da su a jihar.

’Yan bautar ƙasar na cikin waɗanda wasu ’yan bindiga suka sace a ranar Laraba, 26 ga watan Agusta, a kan hanyar Aloma-Egane, da ke Ƙaramar Hukumar Ofu ta Jihar Kogi.

Rahotanni sun ce ’yan NYSC ɗin na kan hanyarsu ne daga sansanin horas da matasa da ke Ƙaramar Hukumar Kolokuma/Opokuma a kihar Bayelsa, zuwa Abuja, bayan kammala shirinsu na horaswa.

Rundunar ’yan sandan ta ce maharan sun fito daga cikin daji ne a kusa da mahadar Ogene Zaria da Onicha-Igo, inda suka tare wasu motocin bas guda biyu tare da yin garkuwa da wasu daga cikin fasinjojin.

Bayan samun kiran neman agaji, jami’an tsaro sun isa wurin inda suka gano motocin bas ɗin da aka bari a wurin, sannan suka fara aikin bincike da tsefe dazuzzukan da ke yankin domin gano waɗanda aka yi garkuwa da su.

Tun da farko, rundunar ta sanar da ceto mutane 11, ciki har da direbobin motocin bas ɗin guda biyu, inda ta ce mafi yawansu ’yan NYSC ne.

A wani sabon aikin ceto kuma, rundunar ta ce an ƙara ceto wasu ’yan bautar ƙasa 10 ta hanyar haɗin gwiwar jami’an ’yan sanda, sojoji da Hukumar DSS.

Rundunar ta bayyana aikin ceto a matsayin wanda aka gudanar cikin haɗin gwiwa tare da amfani da bayanan sirri, domin tabbatar da tsaron waɗanda aka yi garkuwa da su, da kuma tarwatsa ayyukan masu aikata laifin.

Rundunar ta ce aikin bincike da ceto sauran waɗanda ake zargin har yanzu suna hannun masu garkuwa da mutane yana ci gaba, tare da kokarin gano tare da cafke waɗanda suka aikata laifin.

Kwamishinan ’yan sandan Jihar Kogi ya yaba wa jami’an ’yan sanda, sojoji, DSS da sauran jami’an tsaro da suka shiga aikin, bisa jajircewa da ƙwarewar da suka nuna wajen ceto waɗanda aka yi garkuwa da su.

Ya kuma gode wa al’ummar yankunan da abin ya shafa bisa haɗin kai da kuma samar da bayanan sirri da ke taimakawa jami’an tsaro wajen gudanar da ayyukansu.

Rundunar ta ƙara kira ga jama’a da su kasance cikin taka-tsantsan, tare da kai rahoton duk wani mutum ko motsi da suke zargi ga jami’an tsaro mafi kusa, domin taimakawa wajen tabbatar da tsaro a yankin.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Rundunar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Al’umma Su Kiyaye Doka Yayin Bikin Takutaha

Karin Labarai Masu Alaka

Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
Sojin Saman Najeriya Sun Lalata Sansanonin ‘Yan Ta’adda Afrika
Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sanda, Sojoji Da DSS Sun Ceto ‘Yan NYSC Da Aka Sace A Kogi
  • Rundunar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Al’umma Su Kiyaye Doka Yayin Bikin Takutaha
  • RUWASSA Ta Hada Masu Ruwa Da Tsaki Domin Inganta Aiwatar Da Shirin NG-SURWASH
  • Rundunar ’Yan Sandan Bauchi Ta Kama Dattijo Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ’Yar Shekara 8
  • Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata Labarai
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Kamaru Ta Lallasa Malawi 3-0, Ta Lashe Kofin WAFCON Na Farko A Tarihi Wasanni
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
  • Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar Najeriya
  • Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
  • Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.