Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi
Published: January 25, 2026 at 6:41 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ’Yan Sandan jihar Bauchi, ta sanar da kama mutane takwas bayan wani rikici da ya ɓarke tsakanin ma’aikatan karɓar haraji da masu babur a cikin garin Bauchi.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Nafiu Habib, ya fitar, lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, a kusa da kofar Wunti, wato Wunti Gate, bayan Filin Wasan Abubakar Tafawa Balewa.

Rahotannin sirri sun nuna cewa wani mai babur mai suna Ayuba Abdullahi ya samu rauni bayan da wasu ma’aikatan haraji suka kai masa hari saboda ƙin amincewa da bada haraji sau da dama.

Wannan lamari ya fusata takwarorinsa, inda suka gudanar da zanga-zanga a ofishin ƙungiyarsu da ke Muda Lawal.

Rundunar ’yan sanda daga ofisoshin A, B da C, tare da Operation Restore Peace da Rapid Response Squad, sun gaggauta zuwa wurin, inda suka tarwatsa masu zanga-zangar tare da dawo da zaman lafiya.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Jami’an Shige Da Ficen Amurka Sun Harbe Wani Har Lahira
Next Post: Rikicin Siyasa A Jihar Rivers Sakamakon Ayyana Fubara A Matsayin Shugaban APC

Karin Labarai Masu Alaka

Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya Najeriya
Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba Kiwon Lafiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
  • Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Adamu: “Yakar Cin Hanci Daga Tushe Itace Mafita Daya Tilo” Labarai
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya Afrika
  • Iran Ta Tasa Keyar Wani Jirgi Shake Da Mai Sauran Duniya
  • Jam’iyyar ADC Ta Karbi Peter Obi Da Wasu Manyan ‘Yan-Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.