Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi
Published: January 8, 2026 at 5:10 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan jihar Bauchi a Najeriya ta kama wani mutum mai suna Baffaji Abba mai shekaru 28, bisa zargin yi wa ‘yarsa ta cikinsa mai shekaru takwas fyaɗe a ƙaramar hukumar Alkaleri.

A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Nafiu Habib ya fitar, ya bayyana cewa wani ɗan’uwan wanda ake zargin, Baffaji Muhammed, wanda ke zaune a adireshi ɗaya da shi, ne ya kai rahoto zuwa ofishin ‘yan sanda na Alkaleri a ranar 31 ga Disamba, 2025.

Rahoton ya ce lamarin ya faru ne a ranar 30 ga Disamba, 2025, inda wanda ake zargin ya yaudari yarinyar zuwa bandaki sannan ya tilasta mata mu’amala ta jima’i ta hanyar farji da dubura har sau da dama a rana ɗaya, ba tare da amincewarta ba.

Da rundunar ta samu rahoton, tawagar jami’an bincike ƙarƙashin jagorancin CSP Kadiri Danjuma, DPO na Alkaleri, suka je wajen da abin ya faru, suka kai yarinyar asibitin gwamnati na Alkaleri domin samun kulawar gaggawa, sannan suka kama wanda ake zargin.

Yayin bincike, wanda ake zargin ya amsa laifin da aka tuhume shi nan take.

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya umurci Mataimakin Kwamishinan ‘yan sanda mai kula da sashen binciken manyan laifuka (SCID) da ya gudanar da cikakken bincike mai zurfi bisa shaidu da hujjoji.

Ya jaddada kudurin rundunar na ganin an tabbatar da adalci kuma za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Sarkin Kagarko Ya Rasu Yana Da Shekaru 110
Next Post: Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shari’ar Abubakar Malami Ta Kaura Zuwa Sabon Alkali Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
  • Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni
  • Ana Gudanar Da Zanga-Zangar Adawa Da Gwamnati A Kasar Tunisiya Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.