MDD da gwamnatin Somaliya sun fada Ranar talata cewa kimanin ‘yan kasar somaliyan milyan shida da rabi ne suke fuskantar ‘yunwa mai matsanani sakamakon fari, domin ko a makon jiya ma hukumar samar da abinci ta MDD tayi gargadin cewa tallafin abinci da take bayarwa a kasar zai tsaya cik cikin watan Afrilun bana, idan ba an sami karin kudi ba.
A sanarwa ta hadin guiwar MDD da gwamnatin somaliyan suka bayar, sunce fiye da rabin masu fuskantar matsanancin ‘yunwar yara ne, suka ce lamarin ya tilastawa dubban mutane su bar muhallansu suka shiga cikin tantuna a birnin Mogadishu da wasu birane.
A makon jiya, hukumar kula da abinci ta MDD ta ce mutane da suke fuskantar matsananciyar ‘yunwa sun kai milyan hudu da dubu dari hudu, kuma har ta rage yawan wadanda take tallafawa daga mutane milyan biyu da dubu dari biyu, zuwa dubu dari shida kacal daga farkon wannan shekara.


