Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani
Published: February 15, 2026 at 8:53 AM | By: Bala Hassan | Updated: February 15, 2026

Daya daga cikin ‘Yan Jarida 13 da sukayi hatsarin Mota a Bauchi ya Rasuwa

Allah ya karbi rayuwar daya daga cikin ‘Yan Jarida  da sukayi hatsarin Mota a Jihar Bauchi da ke Arewa maso gabas a Najeriya mai suna Khani Ben.

Khani Ben ma’aikacin ne a gidan talabijin na Channels TV ya shahara ta wajan daukar hoto kuma yana wakiltar tashar Channels TV a gidan Gwamnatin Jihar Bauchi.

A ranar Juma’a 6 ga watan Fafurairun 2026 ne tawagar ‘yan Jarida a jihar Bauchi sukayi wani mumunar hatsarin Mota a kan hanyar Yashi zuwa Yelwan Duguri,yayin da zasuje aikin Kaddamar da katafaren Makaranta a garin Yelwan Duguri dake Karamar hukumar Alkaleri a Bauchi wacce hukumar  raya Arewa maso gabas ( NEDC) ta gina.

Ben yana daya daga cikin mutane 14 da hatsarin ya rutsa da su

Tun bayan faruwar lamarin Ben ya samu kansa  cikin mawuyacin hali ganin yana daya daga cikin wadda suka fi samun mumunar rauni sai dai dukkanin su sun samu kulawa daga Gwamnatin Jihar Bauchi da (NEDC) a Babban Asibitin kuyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi inda anan ne rai yayi halinsa.

Rasuwar Mr Ben ya bar babbar gibi a harkar jarida musamman a kafar watsa labari ta Channels TV da ma gidan Gwamnatin Jihar Bauchi inda yake aiki da kuma abokan aikinsa da sauran ma’abota gidan talabijin na Channel TV.

Mr Khani Ben ya kasance haziki kuma jajurtatce wajan aikin jarida da kuma iya mu’amula da al’uma ya rasu ya bar matarsa ​​da ‘ya’yansa biyu.

“Muna mika ta’aziya wa Iyalai, da ‘yan uwansa da hukumar gudanawa na Channels TV da ‘yan Jaridar jihar Bauchi tare da Gwamnatin Jihar Bauchi bisa wannan Babban rashi. GTA Hausa.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana
Next Post: Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
Manchester United Ta Sallami Ruben Amorim Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Masu Zuba Jari A Birnin Paris Afrika
  • Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto Tsaro
  • Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
  • Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
  • Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai
  • Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.