Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci
Published: January 22, 2026 at 7:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 22, 2026

Gwamnatin jihar Gombe ta bai wa Ƙungiyar Maharba da Ƙungiyar Yan Sintiri ta Najeriya (VGN) motoci na aiki, a wani mataki na ƙarfafa ayyukan tsaro da kuma inganta tsaron al’umma a faɗin jihar.

Tallafin ya haɗa da bai wa Ƙungiyar Maharban jihar Gombe motoci biyu kirar Toyota Hilux, ƙarƙashin jagorancin Alhaji Rabiu Baushe (Baushen Gombe), da kuma bai wa Ƙungiyar Yan Sintiri ta Najeriya (VGN), ta jihar Gombe, mota ɗaya kirar Toyota Hilux, ƙarƙashin jagorancin Abubakar Yaro.

Da yake miƙa motocin a madadin Gwamnatin jihar, Darakta-Janar kuma Kwamandan Hukumar Tsaro, Zirga-zirga da Kare Muhalli ta jihar Gombe (GOSTEC)/Operation Hattara, ACP Ibrahim Bappah (Rtd), ya bayyana cewa an bayar da tallafin ne domin ƙarfafa tsaron cikin gida ta hanyar Operation Hattara, tare da zurfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da ƙungiyoyin tsaron al’umma wajen tinkarar ƙalubalen tsaro.

A cewarsa, bayar da motocin na daga cikin tsare-tsaren Gwamnatin jihar Gombe na ƙara wa waɗannan ƙungiyoyi ƙarfi da karsashi wajen gudanar da ayyukansu, da kuma bunƙasa haɗin gwiwar hukumomi domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma a jihar.

“An bai wa shugabannin waɗannan ƙungiyoyi motocin ne domin ƙara musu ƙarfin aiki da kuma tallafa wa ƙoƙarin bai ɗaya na kare rayuka da dukiyoyi a faɗin Jihar Gombe,” in ji ACP Bappah.

Ya kuma yaba wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, bisa jajircewarsa wajen inganta tsarin tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

ACP Bappah ya bayyana tallafin a matsayin wanda ya zo a kan lokaci kuma mai muhimmanci, inda ya ce motocin za su taimaka wajen ƙara saurin kai ɗauki, inganta zirga-zirga, da kuma ƙara ingancin ayyukan tsaro, musamman a matakin ƙananan hukumomi.

A nasa ɓangaren, shugabannin ƙungiyoyin da suka amfana da tallafin sun gode wa Gwamnatin jihar Gombe bisa wannan tallafi, tare da yin alƙawarin amfani da motocin yadda ya dace, bisa ƙa’idoji da dokoki, domin ayyukan tsaro kaɗai.

Sun kuma tabbatar da cewa tallafin zai ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakaninsu da sauran hukumomin tsaro, domin tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da tsaron lafiyar al’ummar jihar Gombe.

Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya
Next Post: Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa

Karin Labarai Masu Alaka

Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
Magoya Bayan Tijjaniyya Zasu Kauracewa Zabe Saboda Kama Sheikh Sani Khalifa Afrika
Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan Afrika
  • Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa Labarai
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
  • Tabbas Za’a Gudanar Da Gasar Firimiya Lig Ta Najeriya Wasanni
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza Labarai
  • Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.