Jose Mourinho ya ƙara ta’azzara takaddamarsa da hukumomin ƙwallon ƙafa na Turkiyya ta hanyar shigar da ƙara a hukumance ga Kotun Kare Hakkin Bil Adama ta Turai (ECHR).
Ɗan ƙasar Portugal ɗin, wanda ake sa ran zai koma ƙungiyar kwallon kafa ta Real Madrid da ke Spain bayan zaɓen shugaban da za a yi a ƙungiyar, ya yi zargin cewa an take masa haƙƙinsa na a lokacin da yake tare da Fenerbahce.
Mourinho Bayan ya bar Fenerbahce a watan Agusta na 2025, ya nemi ECHR a Strasbourg don ƙalubalantar takunkumin ladabtarwa da Hukumar Kwallon Kafa ta Turkiyya (TFF) ta sanya masa.
Shari’ar da aka shigar ta mayar da hankali ne kan martanin da Mourinho ya mayar bayan nasarar da Fenerbahce ta samu a kan Trabzonspor a watan Nuwamba na 2024.
In da aka mishi haramcin wasa ɗaya da kuma tara mai yawa daga hukumomi saboda sukar VAR da hukumomin ƙwallon ƙafa na Turkiyya.
An ci gaba da ɗaukar matakin takunkumin bayan da aka dakatar da daukaka ƙarar kocin, wanda hakan ya sa kocin mai shekaru 63 ya nemi shigar da tasa a kotunan ƙasa da ƙasa.


