Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba”
Published: December 7, 2025 at 9:39 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 8, 2025

­Tsohon kocin Kamaru Marc Brys ya zargi shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Kamaru (FECAFOOT) Samuel Eto’o­, da tsoma baki a zaben ‘yan wasan Indomitable Lions da za su fafata a Gasar Cin Kofin Kasashen Afirka ta 2025,

Brys, wanda aka kora makonni kadan kafin fara gasar da aka tsara daga 21 ga Disamba zuwa 18 ga Janairu, ya yi ikirarin cewa Eto’o ne yake Zaben ‘Yan wasa ba sabon kocin da aka nada David Pagou ne ya dauki nauyin tsara jerin ‘yan wasa na karshe ba.

Kocin dan kasar Belgium ya soki cire manyan taurari, ciki har da mai tsaron gidan Manchester United André Onana da kyaftin dinsa Vincent Aboubakar na dogon lokaci, yana mai bayyana ceresu a matsayin rashin adalci da kuma illa ga damar Kamaru a gasar.

Abubakar shi ne na biyu mafi yawan kwallaye a tarihin kungiyar kwallon kafa ta kasar, inda ya zura kwallaye 45 a wasanni 116.

“Eto’o ya cire manyan ‘yan wasa, kuma Jagorori, domin ya sa ka wanda yake so wannan a bayyane yake “in ji Marc.

Marc ya ce ta yaya za ku iya shiga gasa irin wannan ba tare da mai tsaron gida sananne a duniya ba, ko kuma ba tare da Aboubakar ba?

Waɗannan ‘yan wasa ne masu kwazo, waɗanda ke tsayawa tsayin daka ” in ji Brys a wata hira da wata kafar yada labarai

Brys ya ƙara da sukar halayen Eto’o, yana zargin tsohon ɗan wasan Barcelona da Inter Milan da cewa mai son kai ne.

“Duk wannan ba abin mamaki ba ne a gare ni wajan wanda ke son kai kuma yana tunanin shi ne ya Iya ,” in ji shi.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba
Next Post: Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin

Karin Labarai Masu Alaka

Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni
Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
Arteta, Arsenal Zata Yi Sauye-Sauye A Janairu, Wasanni
Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
  • An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
  • An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
  • Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.