Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki
Published: January 19, 2026 at 9:17 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumomin Uganda sun maido da wasu layukan intanet na kasar cikin daren asabar a bayan da aka ayyana cewa shugaba Yoweri Museveni mai shekaru 81 da haihuwa ya lashe wa’adi na 7 a kan mulki, ma’ana zai shafe shekaru 50 da wani abu yana mulkin kasar.

‘Yan adawa dai sun yi watsi da sakamakon zaben da aka bayyana a zaman na bogi.

Da misalin karfe 11 na daren asabar mutanen kasar ta Uganda suka ce sun fara iya hawa kan intanet, inda wasu kamfanonin sadarwa na kasar suka aike da sako ga kwastomominsu cewa hukumomi sun ba su iznin maido da intanet, amma kuma su ci gaba da toshe hanyoyin hawa kan shafukan sada zumunci.

Hukumar sadarwa ta Uganda ta ce ta bada umurnin katse hanyoyin intanet ne domin dakile yada jita-jita da karairayi da yin magudin zabe. Amma ‘yan hamayya sun soki wannan, suna masu fadin cewa an yi hakan ne kawai domin garkame duk wani fanni na zaben domin tabbatar da cewa Museveni ne ya lashe shi.

A ranar asabar, hukumar zabe ta Uganda ta ce Museveni ya lashe zaben rana4 akhamis da kashi 71 cikin 100 yayin da babban abokin hamayyarsa Bobi Wine ya samu kashi 24 cikin 100.

Labarai, Siyasa

Post navigation

Previous Post: An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya
Next Post: Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa

Karin Labarai Masu Alaka

Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu Afrika
Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
Farashin Mai Ya Cigaba Da Tashi Afrika
Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami Najeriya
  • Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
  • Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
  • Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
  • Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku Wasanni
  • Rasha Takai Sabbin Hare-Hare Akan Wasu Biranen Ukraine Tsaro
  • Ana Gudanar Da Zanga-Zangar Adawa Da Gwamnati A Kasar Tunisiya Siyasa
  • Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.