Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya
Published: January 19, 2026 at 9:08 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumomin tsaron kasar Libya sun kubutar da bakin haure fiye da 200 daga wani kurkukun sirri da aka gina a karkashin kasa a garin Kufra dake yankin kudu maso gabashin kasar, a inda aka tsare su cikin wani mummunan yanayi.

Wasu majiyoyin tsaro biyu a kasar sun ce hukumomi sun gano wannan kurkuku da aka gina mai zurfin mita 3 a karkashin kasa a garin na Kufra wanda wani madugun ‘yan safarar mutane na Libya yake gudanar da shi.

Daya daga cikin majiyoyin yace har yanzu ba a kama mutumin da ya gina yake gudanar da wannan kurkuku na sirri ba.

Majiyar ta ce wasu daga cikin wadannan bakin haure sun shafe shekaru 2 suna daure a ciki. Daya majiyar kuma ta ce sumamen da aka kai ya bankado laifi na cin zarafin bil adama mafi muni da aka taba ganowa a yankin.

Bakin hauren da aka kubutar daga wannan bala’i sun fito ne daga kasashen kudu da hamadar Sahara, kuma akasarinsu daga kasashen Somaliya da Eritrea, kuma sun hada da mata da yara kanana. Garin Kufra yana gabashin Libya, kimanin kilomita 1700 daga Tripoli, babban birnin kasar.

Tun bayan da kungiyar kawancen tsaro ta NATO ta taimaka wa ‘yan tawaye wajen kawarwa da kashe shugaba Muammar Gaddafi a 2011, Libya ta zamo zangon safarar bakin hauren dake tserewa daga yake-yake da talauci, wadanda ke bi ta wannan hanya mai hatsarin gaske ta cikin hamada bisa zummar samun hanyar kaiwa kasashen Turai.

A makon da ya shige ma, an gano gawarwakin bakin haure su 21 a wani ramin da aka haka aka binne su a yankin na gabashin Libya, inda aka samu wasu da suka kubuta da rayukansu da aka ga alamun an gana musu azaba kafin a sake su

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain
Next Post: Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki

Karin Labarai Masu Alaka

Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai
Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa Afrika
Kenya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kasar Rasha Afrika
Tarkacen Makamai Masu Linzami Sun Lalata Gidaje Da Wuraren Kasuwancin Palasdinawa Afrika
Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH Afrika
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
  • ‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.