Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya
Published: January 19, 2026 at 9:08 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumomin tsaron kasar Libya sun kubutar da bakin haure fiye da 200 daga wani kurkukun sirri da aka gina a karkashin kasa a garin Kufra dake yankin kudu maso gabashin kasar, a inda aka tsare su cikin wani mummunan yanayi.

Wasu majiyoyin tsaro biyu a kasar sun ce hukumomi sun gano wannan kurkuku da aka gina mai zurfin mita 3 a karkashin kasa a garin na Kufra wanda wani madugun ‘yan safarar mutane na Libya yake gudanar da shi.

Daya daga cikin majiyoyin yace har yanzu ba a kama mutumin da ya gina yake gudanar da wannan kurkuku na sirri ba.

Majiyar ta ce wasu daga cikin wadannan bakin haure sun shafe shekaru 2 suna daure a ciki. Daya majiyar kuma ta ce sumamen da aka kai ya bankado laifi na cin zarafin bil adama mafi muni da aka taba ganowa a yankin.

Bakin hauren da aka kubutar daga wannan bala’i sun fito ne daga kasashen kudu da hamadar Sahara, kuma akasarinsu daga kasashen Somaliya da Eritrea, kuma sun hada da mata da yara kanana. Garin Kufra yana gabashin Libya, kimanin kilomita 1700 daga Tripoli, babban birnin kasar.

Tun bayan da kungiyar kawancen tsaro ta NATO ta taimaka wa ‘yan tawaye wajen kawarwa da kashe shugaba Muammar Gaddafi a 2011, Libya ta zamo zangon safarar bakin hauren dake tserewa daga yake-yake da talauci, wadanda ke bi ta wannan hanya mai hatsarin gaske ta cikin hamada bisa zummar samun hanyar kaiwa kasashen Turai.

A makon da ya shige ma, an gano gawarwakin bakin haure su 21 a wani ramin da aka haka aka binne su a yankin na gabashin Libya, inda aka samu wasu da suka kubuta da rayukansu da aka ga alamun an gana musu azaba kafin a sake su

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain
Next Post: Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki

Karin Labarai Masu Alaka

Farmakin Da Aka Kai Makarantar Mata A Iran Yayi Ajalin Yara Da Dama Afrika
Shugaban Amurka Donald Trump Yace Bai Taba Shiga Jirgin Jeffrey Epstein Ba Labarai
Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa Amurka
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur Afrika
  • Shugaba Trump Da Gwamnan Minnesota Zasu Sassautawa Bakin Haure Amurka
  • Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.