Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya
Published: December 26, 2025 at 5:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Trump ya ce Amurka ta kai “hare-hare masu yawa” masu kisa kan ‘yan ta’adda a Najeriya.

Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya ce a ranar Alhamis sojojin Amurka sun kai munanan hare-hare kan ‘yan ta’addar Daular Musulunci (ISIS) a Arewa maso Yammacin Najeriya, tare da yin barazanar ci gaba da kai hare-hare idan ‘yan ta’addan suka ci gaba da kashe kiristoci.

Shugaban ya bayyana hakan ne a shafinsa na X inda ya ƙara da cewa Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka ta aiwatar da hare-hare masu nasara da dama.

Ya rubuta cewa, “Yau da daddare, bisa umarni na a matsayi na na Babban Kwamandan Sojojin Amurka ta kaddamar da wani mummunan hari mai ƙarfi kan ‘yan ta’addar ISIS a Arewa maso Yammacin Najeriya, waɗanda suka dade suna kai hari tare da kashe Kiristoci marasa laifi.

“A baya na yi gargaɗi ga waɗannan ‘yan ta’adda cewa idan ba su daina kisan Kiristoci ba, za su fuskanci mummunan sakamako, kuma a daren yau hakan ta faru.

“Ma’aikatar Yaƙi ta aiwatar da hare-hare masu tsari da nagarta da dama, irin waɗanda Amurka kaɗai ke iya aiwatarwa.

“A ƙarƙashin jagoranci na, ƙasar mu ba za ta bari ta’addancin Musulunci mai tsatsauran ra’ayi ya bunƙasa ba.

“Allah Ya albarkaci sojojin mu, kuma Barka da kirsimeti ga kowa, har da ‘yan ta’addar da aka kashe, waɗanda za su ƙaru idan suka ci gaba da kisan Kiristoci.”

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya
Next Post: Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai
Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup  Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka Afrika
  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
  • Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025. Wasanni
  • Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Tura Rundunar Tsaron Sham Zuwa Kakarshin Ikon Kurdawa Labarai
  • Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Zata Binciki Kasar Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.