Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero
Published: April 19, 2026 at 4:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta kaddamar da ginin sabuwar tashar samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana mai karfin megawat daya (1MW) a Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK), domin kawo karshen matsalar duhu da tsadar makamashi da ke addabar jami’ar.

Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Kasa (ECN), Dokta Mustapha Abdullahi, shi ne ya bayyana hakan yayin taron kaddamar da aikin da aka gudanar a cikin jami’ar.

Dokta Abdullahi ya bayyana cewa wannan aiki ya zo da wata sabuwar fasaha ta musamman wadda ko kura ta yi yawa ko kuma hadari ya rufe rana, na’urorin za su ci gaba da bayar da wuta. Haka kuma, akwai tsarin sanya ido ta kwamfuta ko wayar salula domin sanin yadda wutar ke gudana.

“Wannan ba wai kawai sanya fanoni (panels) ba ne; tsari ne da aka hada shi da inbata (inverters), batura da tirasfoma wadanda ke aiki tare cikin tsari daya,” in ji shi.

Ya kara da cewa an riga an kawo muhimman kayayyaki kamar batura na ‘Lithium’ da fanonin hasken rana zuwa jami’ar, kuma an riga an amince da kudaden aikin, don haka ’yan kwangila za su shiga aiki gadan-gadan.

Wannan sabon aiki na zuwa ne daidai lokacin da ake kokarin farfado da wata tsohuwar tashar hasken rana mai karfin 3.5MW wadda tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo, ya kaddamar a shekarar 2019.

Tsohon aikin, wanda aka kashe masa Naira biliyan 5.6, ya daina aiki ne tun a shekarar 2021, lamarin da ya jefa jami’ar cikin duhu da kuma dogaro da injinan dizal masu cin kudi.

Da yake nasa jawabin, Shugaban Jami’ar BUK, Farfesa Haruna Musa, ya dora alhakin lalacewar tsohon aikin a kan rashin saka kwararrun injiniyoyin jami’ar yayin gudanar da shi. Sai dai ya ba da tabbacin cewa a wannan karon za su sanya ido sosai.

“Za mu tabbatar mun kula da wannan aiki yadda ya kamata. Inda aka zaba don kafa wannan tasha wuri ne da muke fuskantar kalubalen tsaro, don haka zai taimaka mana kwarai,” in ji Farfesa Musa.

Dokta Mustapha Abdullahi ya bayyana cewa wannan megawat daya da aka fara da shi a BUK matakin gwaji ne (pilot phase), inda akwai shirin kara karfin wutar zuwa megawat 4.5 nan gaba.

Sannan ya kara da cewa wannan bangare ne na babban shirin gwamnati na raba megawat 150 na hasken rana a fadin jihohi 36 na Najeriya da kuma birnin tarayya Abuja, domin samar da wuta mai rahusa ga al’umma.

Sama da 40,000 ne za su amfana da wannan haske wanda zai Saukaka binciken kimiyya da kyautata rayuwar dalibai a ajujuwa da dakunan kwanansu.

Afrika, Kimiya, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC
Next Post: Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba Amurka
Jam’iyar APC A Jihar Gombe Ta Tsayar Da Jamilu Isiyaku Gwamna Takarar Gwamna Afrika
An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika
  • Paparoma Leo: Zai Kai Ziyara Ƙasar Angola Labarai
  • Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
  • Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.