Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar
Published: December 11, 2025 at 6:37 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Bauchi ta amince da fitar da naira miliyan 97 domin sabunta masana’antar sarrafa nama ta jihar da ke Bauchi, a wani bangare na kokarinta na farfado da harkokin kiwo da sarrafa nama a jihar.

Kwamishinan Ma’aikatar kyautata Kiwo, Dr. Musa Lukshi ne ya bayyana hakan yayin wani ziyarar duba ci gaban aikin da ake yi a masana’antar.

Ya ce kudaden da Gwamna Bala Abdulkadir Muhammad ya fitar da gaggawa, alama ce ta kudurin gwamnati na inganta darajar sarkar kiwo da kara tabbatar da inganta abinci da ake samarwa al’umma.

Dr. Lukshi ya ce aikin sabuntawar zai hada da girka kayan aiki na zamani, wanda zai taimaka wajen ingantawa tare da tsaftace tsarin aiki da kuma ingancin nama da ake samarwa.

Ya kara da cewa bayan kammala aikin, masana’antar za ta samar da guraben ayyukan yi ga matasa da sauran ma’aikata, tare da bunkasa tattalin arziki da kudaden shiga ga jihar.

Masu kiwo da sauran masu ruwa da tsaki sun bayyana jin dadinsu da shirin, suna masu fatan zai samar da kasuwa mai dorewa, inganta farashi, da rage asarar da ake fuskanta bayan yanka.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar
Next Post: Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas Labarai
Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika
Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Gangar Mai Yayi Gagarumar Fadi A Kasashen Duniya Labarai
  • Kama Muhyi Magaji Siyasa ce Kawai Inji Gwamnatin Kano Labarai
  • Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya
  • Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
  • Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
  • Liverpool Tayi Rashin Nasara A Wasanni Tara Wasanni
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran Amurka
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.