Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato
Published: May 8, 2026 at 12:52 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 8, 2026

Mummunan lamari na kisan mutane da lalata dukiyoyi a jihar Filato ya kasance da matukar damuwa ga al’ummar jihar dake hankoron samun mafita.

Rahoton da wani komiti da gwamnatin jihar Filato ta kafa a shekara ta dubu biyu da ishirin da biyar, karkashin shugabancin Janar Nicholas Rogers ya bayyana cewa daga shekara ta dubu biyu da daya zuwa shekara ta dubu biyu da ishirin da biyar, mutane dubu goma sha daya da dari bakwai da arba’in da tara ne suka rasa ransu, dalilin rikice-rikicen da suka shafi neman wawure filin zama, da na noma da kiwo, ayyukan ‘yan bindiga da bata gari, rikice-rikicen da ake dangantawa da addini da kabilanci da sauransu.

Rahoton yace lamarin ya shafi yankuna dari hudu da ishirin a kananan hukumomi goma sha uku na jihar.

Tun bayan mika rahoton wa gwamnatin jihar Filato, al’ummar jihar, musamman wadanda ke karkara, sun ci gaba da samun kansu cikin wannan mummunan yanayi ba tare da sassauci ba.

A baya-bayan nan, wani lamari dake nema zama ruwan dare a wassu sassan jihar shine yadda matasa ke tare hanya, bayan kaiwa hari a kauye, cikin fushi su kashe ko jikkata matafiya da basu san hawa da sauka ba.

Mai fashin baki kan lamura, musamman a kafar sada zumunta, Steve Davou Damar yace babu addini ko dabi’a da ta goyi bayan kisan wanda bashi da laifi.

Shima shugaban rikon kwarya na gamayyan kungiyoyin matasa a Najeriya, Barista Buhari Ibrahim Shehu yace rashin sanin doka a bangaren matasa na daga dalilan da yasa batun tare hanya a kashe mutane ke ci gaba da aukuwa.

A bangare guda kuwa gwamnatin jihar Filato ta sha alwashin daukan mataki kan duk wanda ya tare hanya da sunan ramako.

Sakataren gwamnatin jihar Filato, Samuel Jatau yace wannan salo da al’ummar Filato ke yi na tare matafiya a kan hanyar gwamnati ba daidai bana, kuma gwamnatin zata dauki mataki.

Duk da shike wannan ba shine karo na farko da gwamnatin ke ikirarin daukan mataki ba, domin a kwanakin baya an jiyo gwamnan jihar Caleb Mutfwang na ikirarin kama duk wani basarake da matasan yankinsa suka tare hanya, to sai dai ko gwamnatin ta kama wani ko a’a, salon tare hanya da keyi a wassu sassan jihar na neman zama nomal, bi ma’ana, lamari na yau da kullum.

Daga Jos Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/05/AUD-20260508-WA0035.mp3
Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Shiga Takara Wa’adi Na Biyu
Next Post: Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata

Karin Labarai Masu Alaka

Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga Afrika
Kasar Iran Zata Kai Hare Haren Ramuwar Gayya Isra’ila Afrika
Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Namibiya Tayi Watsi Da Yarjejeniya Tsakanin Ta Da Kamfanin Total Labarai
  • Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari Labarai
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.