Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci
Published: December 22, 2025 at 2:12 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Najeriya da ƙasar Amurka sun sanya hannu kan yarjejeniyar dala biliyan 5.1 don inganta asibitocin Kiristoci

Amurka da gwamnatin tarayyar Nijeriya sun kulla yarjejeniyar haɗin gwiwar kiwon lafiya ta tsawon shekaru biyar domin ƙarfafa tsarin kula da lafiya a Nijeriya.

Yarjejeniyar, wadda aka sanya hannu a ranar Asabar, ta tanadi kusan dala biliyan 2.1 daga Amurka, yayin da Nijeriya ta yi alƙawarin zuba kusan dala biliyan 3 daga cikin gida.

A cewar sanarwar da aka fitar, yarjejeniyar za ta mayar da hankali ne kan yaƙi da cututtuka kamar HIV/AIDS, tarin fuka, zazzabin cizon sauro, shan inna, da kuma rage mace-macen mata masu juna biyu da yara, waɗanda ke ci gaba da zama manyan ƙalubalen lafiyar jama’a a ƙasar.

Wani muhimmin ɓangare na yarjejeniyar shi ne tallafi na musamman ga cibiyoyin kiwon lafiya na addinin Kirista, waɗanda ke da kusan cibiyoyi 900 a faɗin Nijeriya.

Waɗannan cibiyoyin, da dama daga cikinsu suna aiki a yankunan karkara da wuraren da ke da ƙarancin ayyuka, suna ba da agaji ga sama da kashi 30 cikin 100 na al’ummar ƙasar.

Jami’an Amurka da na Nijeriya sun ce haɗin gwiwar za ta faɗaɗa damar samun ayyukan lafiya, ƙarfafa tsaron lafiya, da kuma gina tsarin kiwon lafiya mai ɗorewa sannan sun ƙara da cewa yarjejeniyar na nuna ƙudirin Nijeriya na ƙara kashe kuɗaɗe a fannin lafiya da kuma inganta sa ido kan cututtuka da martani ga ɓarkewar annoba.

Sai dai kuma, yarjejeniyar ta jawo ra’ayoyi mabanbanta daga jama’a, inda wasu ke yaba wa shigowar tallafin kuɗi, yayin da wasu ke nuna damuwa kan mai da hankali ga cibiyoyin addini a ƙasa mai tsarin mulki na zamani.

Amurka, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kasashen AES Sun Buɗe Gidan Talabijin Na Bai Daya
Next Post: NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari

Karin Labarai Masu Alaka

An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe Afrika
Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu Najeriya
An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu Labarai
Jihar Kano Tayi Rashin ‘Yan Majalisu Biyu Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama Najeriya
  • An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Jaddada Shirin Yaƙi Da Munanan Dabi’u Afrika
  • Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika
  • Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina Afrika
  • Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.