Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari
Published: December 22, 2025 at 4:35 PM | By: Mahmud Kwari | Updated: December 22, 2025

Hukumar NDLEA dake ayyukan hana sha da fataucin miyagun kwayoyi da ababen sanya maye a Najeriya tace tana tsananta bincike akan ‘yan matan nan guda biyu da ak damke yayin da sukayi yunkurin kai kwayar Tramadol ga wasu mutane dake tsare a gidan gyaran hali a Kano.

Jami’an hukumar kula da gidan gyaran halin ne suka damke ‘yan matan Maryam Ali ‘yar shekaru 19 da Hauwa Musa mai shekaru 20 a yayin binciken masu ziyarar daurarru a gidan gyaran hali na Goron Dutse a Kano.

Maryam Ali da Hauwa Musa sun boye kwayoyin tramadol din ne a cikin gurasa da sauran kayayyakin cimaka da suka dauko domin kaiwa samarin su dake daure.

DSP, Misbahu Lawan, kakakin hukumar kula da gyaran hali ta Najeriya shiyyar Kano yace damke ‘yan matan na daga cikin samakon tsauraran matakan da suke dauka akan masu ziyarar daurarru.

Yanzu haka dai hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya ta karbi ragamar gudanar da binciken kwakwaf akan wadannan ‘yan mata Maryam Ali da Hauwa Musa.

ASP, Sadiq Muhammad Maigatari, dake zaman kakakin hukumar ta NDLEA a Kano, yace Maryam Ali, guda cikin ‘yan Matan ta shaida musu cewa, tana shirin kaiwa saurayin ta kwayoyin tramadol da aka kamata dasu ne, wanda ke daure a can gidan gyran hali na Goron Dutse a Kano. Tace ita-ma tana amfani da nau’ikan kayayyakin san maye, irin su Codeine da tabar Wiwi.

Wannan yunkurin ‘yan mata domin safarar kwayoyi zuwa cikin gidajen da ake tsare da masu laifi, na kara fito da jan aikin dake gaban gwamnati da hukumominta wajen yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyi da ababen sanya maye a Najeriya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci
Next Post: Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki

Karin Labarai Masu Alaka

Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin Afrika
Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma Afrika
An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
Gwamnatin Najeriya Ta Jaddada Aniyarta Ta Daƙile Yaɗuwar Makamai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Kasar Tunisiya Ya Tsawaita Dokar Da Baci A Kasar Labarai
  • Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
  • Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa Afrika
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
  • Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata Afrika
  • Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.