Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari
Published: December 22, 2025 at 4:35 PM | By: Mahmud Kwari | Updated: December 22, 2025

Hukumar NDLEA dake ayyukan hana sha da fataucin miyagun kwayoyi da ababen sanya maye a Najeriya tace tana tsananta bincike akan ‘yan matan nan guda biyu da ak damke yayin da sukayi yunkurin kai kwayar Tramadol ga wasu mutane dake tsare a gidan gyaran hali a Kano.

Jami’an hukumar kula da gidan gyaran halin ne suka damke ‘yan matan Maryam Ali ‘yar shekaru 19 da Hauwa Musa mai shekaru 20 a yayin binciken masu ziyarar daurarru a gidan gyaran hali na Goron Dutse a Kano.

Maryam Ali da Hauwa Musa sun boye kwayoyin tramadol din ne a cikin gurasa da sauran kayayyakin cimaka da suka dauko domin kaiwa samarin su dake daure.

DSP, Misbahu Lawan, kakakin hukumar kula da gyaran hali ta Najeriya shiyyar Kano yace damke ‘yan matan na daga cikin samakon tsauraran matakan da suke dauka akan masu ziyarar daurarru.

Yanzu haka dai hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya ta karbi ragamar gudanar da binciken kwakwaf akan wadannan ‘yan mata Maryam Ali da Hauwa Musa.

ASP, Sadiq Muhammad Maigatari, dake zaman kakakin hukumar ta NDLEA a Kano, yace Maryam Ali, guda cikin ‘yan Matan ta shaida musu cewa, tana shirin kaiwa saurayin ta kwayoyin tramadol da aka kamata dasu ne, wanda ke daure a can gidan gyran hali na Goron Dutse a Kano. Tace ita-ma tana amfani da nau’ikan kayayyakin san maye, irin su Codeine da tabar Wiwi.

Wannan yunkurin ‘yan mata domin safarar kwayoyi zuwa cikin gidajen da ake tsare da masu laifi, na kara fito da jan aikin dake gaban gwamnati da hukumominta wajen yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyi da ababen sanya maye a Najeriya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci
Next Post: Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
  • Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
  • Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram Najeriya
  • Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
  • Amurka Da Kasashen Yamma Suna Cigaba Da Kai Ruwa Rana Akan Nukiliyar Iran Afrika
  • Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Namibiya Tayi Watsi Da Yarjejeniya Tsakanin Ta Da Kamfanin Total Labarai
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.