An fara jigilar alhazan Najeriya zuwa gida bayan kammala manyan ayyukan Hajjin shekarar 2026, inda jirgi na farko ya tashi daga birnin Jeddah zuwa Abuja a yau Laraba, 3 ga watan Yuni.
Bayanan da Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta fitar ta hannun Cibiyar Kula da Ayyuka da Sadarwa (Command and Control Center) da ke Makkah sun nuna cewa jirgin MaxAir mai lamba NGL267 ya tashi daga filin jirgin sama na Jeddah da misalin karfe 9:27 na safe dauke da alhazai 560 daga Jihar Nasarawa.
Da wannan jigila, jimillar alhazan da aka dawo da su Najeriya ta kai 560, yayin da aka gudanar da jirgi na daya a ranar farko ta dawowar alhazai.
Ana sa ran kamfanonin jiragen saman da ke aikin Hajji za su ci gaba da jigilar dubban alhazan Najeriya daga Saudiyya zuwa jihohinsu a cikin makonni masu zuwa, yayin da NAHCON ke sa ido kan aikin domin tabbatar da dawowa cikin tsari da nasara.


