Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya
Published: June 3, 2026 at 1:17 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta a Najeriya (INEC), ta ce ta fara bincike kan zargin fitar da bayanan wani ɗan takara daga kundin rajistar masu kaɗa ƙuri’a (CVR), yayin da Hukumar Tsaro ta Farin Kaya, (DSS), ita ma ta fara nata binciken.

INEC ta bayyana cewa binciken farko ya nuna babu wani kutse daga waje ko harin na’ura mai kwakwalwa da ya shiga tsarin bayananta. Sai dai an samu damar shiga bayanan ne ta hanyar sahihan bayanan shiga da aka bai wa wasu jami’an rajistar masu zaɓe, amma aka fitar da bayanan ba tare da izini ba.

Hukumar ta ce ta gano asusun da aka yi amfani da shi wajen shiga bayanan, kuma tana binciken ko an karya dokokin tsaro da kariyar bayanai. Ta kuma tabbatar da cewa lamarin bai shafi bayanan sama da masu zaɓe miliyan 90 da ke cikin kundinta ba.

Sai dai ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya ce bayanin da INEC ta fitar ya ƙara haifar da tambayoyi fiye da amsoshi. Ya buƙaci a yi cikakken bincike domin gano yadda bayanan da ke cikin tsarin da aka killace suka kai hannun wasu ‘yan siyasa.

Atiku ya ce rashin samun kutse daga waje ba ya rage girman lamarin, domin hakan na nuna yiwuwar matsalar ta fito daga cikin tsarin hukumar. Ya kuma yi maraba da binciken DSS, yana mai cewa dole ne a gudanar da shi cikin adalci ba tare da nuna son kai ba.

Takaddamar ta samo asali ne bayan mai taimaka wa Ministan Abuja kan harkokin yaɗa labarai, Lere Olayinka, ya wallafa bayanan rajistar zaɓe na fitaccen jarumin Nollywood, Emeka Ike. Jarumin ya yi zargin cewa an karya masa haƙƙin sirri, tare da barazanar ɗaukar matakin shari’a kan lamarin.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai
Next Post: An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
Jirgin Sama Ya Fadi A Kano Labarai
Amurka Zata Bada Gudunwa Ga Masu Zanga-Zanga A Iran Sauran Duniya
Gwamnatin Jihar Neja Ta Soke Lasisin Mallakar Wasu Manyan Filaye A Jihar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yobe Ta Sake Jaddada Ƙudirin Rage Mutuwar Yara Afrika
  • Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
  • Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
  • An Bukaci Sabbin Shugabanni Su Yi Jagoranci Nagari da Inganta Ayyukan Jama’a Labarai
  • Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato Bidiyo
  • Farashin Mai Ya Ragu A Kasuwar Duniya Amurka
  • Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.