Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Ministan Harkokin Wajen Iran Yagana Da Shugaban Sa’ido Akan Nukiliya
Published: February 16, 2026 at 6:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin wajen Iran ya gana da shugaban hukumar sa ido kan makamashin nukiliya na Majalisar Dinkin Duniya a Ranar Litinin, kafin ci gaba da tattaunawa tsakanin Iran din da Amurka don shawo kan rikici game da makaman Nukiliya na Iran, inda alamu kadan ke nunawa za’a samu daidaito, ga kuma barazanar daukan matakin soja dake tunkarowa.

A makon da ya gabata ne, fadar Washington ta aike da jirgin ruwa mai dakon jiragen yaki a karo na biyu zuwa gabas ta tsakiya. Ita kuma kasar Iran a yau Litinin ta fara gabatar da atisayen soja a mashigar Hormuz, wanda gabar ruwa ne mai muhimmanci ga kasashen waje, kuma ta nan ake fitar da man fetur daga kasashen larabawa na tekun Fasha, wadanda suke ta rokon a bi hanyar diplomasiyya don kawo karshen rikicin.

Amurka da Iran sun sake zama don tattaunawa kan shirin Iran na nukiliya, wanda fadar Washington da sauran kasashen yamma ke ganin Iran na yi ne don gina makaman nukiliya. Abinda Iran din ta musanta.

Farashin man fetur bai samu wani sauyi mai yawa ba a ranar Litinin, yayin da masu sa hannun jari suke duba yadda tattaunawa tsakanin Iran da Amurka zata shafi kasuwar man, da kuma sa ran da ake na samun karuwar man daga kasashe masu arzikin man fetur na OPEC.

Afrika, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi
Next Post: Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Kasar Ghana Ta Rage Farashin Cocoa Afrika
  • Mataimakin Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wasu Wakilai Amurka
  • Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza Afrika
  • Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Birai Afrika
  • Isra’ila Takai Hare Hare Birnin Tehran Afrika
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • Kasar Amurka Ta Sayi Kamfanin Sada Zumunci Na Tik-Tok Amurka
  • Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.