Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Ministan Harkokin Wajen Iran Yagana Da Shugaban Sa’ido Akan Nukiliya
Published: February 16, 2026 at 6:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin wajen Iran ya gana da shugaban hukumar sa ido kan makamashin nukiliya na Majalisar Dinkin Duniya a Ranar Litinin, kafin ci gaba da tattaunawa tsakanin Iran din da Amurka don shawo kan rikici game da makaman Nukiliya na Iran, inda alamu kadan ke nunawa za’a samu daidaito, ga kuma barazanar daukan matakin soja dake tunkarowa.

A makon da ya gabata ne, fadar Washington ta aike da jirgin ruwa mai dakon jiragen yaki a karo na biyu zuwa gabas ta tsakiya. Ita kuma kasar Iran a yau Litinin ta fara gabatar da atisayen soja a mashigar Hormuz, wanda gabar ruwa ne mai muhimmanci ga kasashen waje, kuma ta nan ake fitar da man fetur daga kasashen larabawa na tekun Fasha, wadanda suke ta rokon a bi hanyar diplomasiyya don kawo karshen rikicin.

Amurka da Iran sun sake zama don tattaunawa kan shirin Iran na nukiliya, wanda fadar Washington da sauran kasashen yamma ke ganin Iran na yi ne don gina makaman nukiliya. Abinda Iran din ta musanta.

Farashin man fetur bai samu wani sauyi mai yawa ba a ranar Litinin, yayin da masu sa hannun jari suke duba yadda tattaunawa tsakanin Iran da Amurka zata shafi kasuwar man, da kuma sa ran da ake na samun karuwar man daga kasashe masu arzikin man fetur na OPEC.

Afrika, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi
Next Post: Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
Tinubu Na Kokarin Rage Tsadar Sufuri Ta Hanyar Shirin CNG Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci Afrika
Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika
Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
  • Kasar Ghana Ta Bayyana Fataucin Bayi A Matsayin Babban Laifi Afrika
  • An Gudanar Da Tiyatar Ido Kyauta A Gombe Afrika
  • Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
  • Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
  • Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.