Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha
Published: December 30, 2025 at 5:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar Litinin, Rasha ta zargi ukraine da kai hari kan gidan shugaban Rasha Vladimir Putin, daga nan tayi alkwarin zata dauki fansa duk da cewa bata nuna wata shaidar harin ba, tuni dai Ukraine tayi watsi da zargin, tana mai cewa Rasha tana kokarin tayi kafar ungulu akan shawarwarin neman kawo karshen yaki da kasashen biyu suke yi.

Musayar zazzafar kalamai tsakanin makwabtan kasashen biyu ranar litinin, ciki harda ikirarin da Rasha tayi cewa harin yasa zata sake nazarin matsayar ta a shawarwarin neman kawo karshen yakin, wadda hakan zai maida hanun agogo baya a yunkurin wanzar da zaman lafiya tsakanin kasashen biyu.

Shugaba Donad Trump na Amurka yace Putin ya gaya masa batun harin, da suka yi magana ta wayar tarho ranar litinin da safe, yace labarin ya bakanta masa rai, duk da haka yace har yanzu yana ganin an kusa a cimma matsayar da zata wanzar da zaman lafiya a rikici tsakanin kasashen biyu.

Da aka tambaye shi ko hukumomin leken asirin Amurka suna da shaidar zargin harin da Putin yayi, shugaba Trump, yace ‘Zamu mu bincika mu gani.”

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Trump Yayi Barazanar Goyon Bayan Hari Akan Kasar Iran
Next Post: Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan

Karin Labarai Masu Alaka

Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
Trump Yayi Barazanar Goyon Bayan Hari Akan Kasar Iran Labarai
An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
An Kaiwa Sojojin Ghana Hari A Lebanon Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
  • Iran Da Amurka Sun Gindayawa Juna Ka’idojin Tsagaita Wuta Afrika
  • Harkar Zirga Zirgar Jiragen Sama Ya Bunkasa A Kenya Afrika
  • An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.