Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u
Published: December 14, 2025 at 11:08 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC da Shugaba Bola Tinubu sun fara aiwatar da wata babbar dabarar siyasa domin tabbatar da nasara a zaben shugaban kasa na 2027, ta hanyar karfafa ikonsu a yankunan Kudu da Arewa ta Tsakiya.

Majiyoyi daga APC sun ce an fara shirin tun fiye da watanni biyar da suka wuce, bayan rahotannin sirri sun nuna yiwuwar barazana daga Arewa da kuma bullowar hadakar jam’iyyun adawa.

Shirin na da nufin rage tasirin adawar Arewa ta hanyar samun dunkulen kuri’u daga Kudu da Arewa ta Tsakiya.

Kungiyoyin Arewa da wasu fitattun ‘yan siyasa sun nuna rashin jin dadi da mulkin Tinubu, lamarin da ya sa APC ke kokarin karbe dukkan jihohin Kudu a 2027.

A zaben 2023, jam’iyyun adawa sun lashe jihohi da dama a Kudu da Arewa ta Tsakiya, ciki har da Lagos da Abuja.

APC ta ce tana amfani da kulla kawance, jawo hankalin manyan jiga-jigai da kuma tasirin gwamnatin tarayya domin kwato wadannan jihohi.

Jam’iyyar ta yi imanin cewa samun cikakken goyon bayan Kudu zai bai wa Tinubu gagarumar dama ta lashe zabe wa’adi na biyu.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi

Karin Labarai Masu Alaka

Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
Kasar Faransa Ta Karyata Cire Afirka Ta Kudu Daga G7 Afrika
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
  • Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
  • Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
  • An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.