Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Magoya Bayan Obi Sun Yi Tutsu Gabanin Zaben 2027
Published: March 21, 2026 at 4:08 AM | By: Nasiru Adamu Elhikaya | Updated: March 21, 2026

Manyan Magoya Bayan Obi Sun Fice Da Kafa Kungiyar Movement Nigeria

Wasu daga manyan jami’an siyasar dan takarar adawa a Najeriya wato Peter Obi sun barranta daga tafiyar da kafa wata kungiyar cimma sabon muradi don babban zaben 2027.

‘Yan siyasar sun koka cewa tafiyar ta su mai taken OBIDIENTS ta sauka daga kan manufofin kare martabar dimokradiyya

“A matsayinmu na masu tafiyar farar hula mun yi amanna cewa tsarin siyasa na cikin abubuwan da kan kawo cigaban kasa, za mu dage wajen hulda da wadanda su ka cancanta, cikin gaskiya da bin ka’ida ga sauran tafiyar dimokradiyya ko jam’iyyun siyasa. Wannan tafiya ce ta ma’aikata da ke fafutuka..” Inji madugun tafiyar mai taken MOVEMENT Nigeria Prince Kolade Ademola.

Ademola ya ce ba lallai a yanzu su na da wanda za su marawa baya ga babban zaben ba amma za su goyi bayan duk wanda su ka ga ya dace da tafiyarsu kuma ya karfafa cewa lokaci bai kure mu su ba.

‘Yan sabuwar tafiyar maza da mata sanya da riguna da hulunan hana-sallah masu tambarin kungiyar, na nuna rashin daidaito da tuntubar da ta dace ya sa su kaucewa tafiyar Peter Obi wanda ya zo na uku a yawan kuri’a a zaben 2023.

Mataimakin sakataren jam’iyyar LEBA na kasa wacce Obi ya yi ma ta takara Dokta Joseph Liran ya ce sam ba don dalilin kaurar Obi zuwa jam’iyyar ADC ya sa su barranta daga tafiyar ba “Obi ya na da ‘yancin shiga kowace jam’iyya mu ma mu na da namu ‘yancin”

Shi ma ma’ajin jam’iyyar LEBA Malam Hamisu Santuraki ya ce ba za su ce dole sai muradun LEBA za a bi ba a madadin ra’ayin jama’ar kasa.

Hakanan Santuraki ya ce sun kawo karshen takaddamar shugabancin jam’iyyar ta LEBA bayan hukuncin kotun koli da ya kawar da jagorancin Julius Abure.

Irin wannan tafiya ba sabon abu ba ne a shekarar siyasa inda ‘yan siyasar ke duba

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/OBIDIENTS-DUMP-OBI-START-NEW-MOVEMENT.mp3

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya
Next Post: Hawan Sallah Daga Masarautar Kaltungo

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai
Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda Siyasa
Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu Zai Gabatar Da Jawabi ga Shugabannin Duniya A Taron UNGA Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
  • Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika
  • Sama Da Zawiyya 100 Ne Suka Samu Tallafin Kayan Abinci Daga Al’mustapha Haji Sufi Labarai
  • Mamakon Ruwan Sama Da Iska Ya Hallaka Mutane Uku A Jihar Yobe Labarai
  • Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.