Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika

Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC
Published: June 27, 2026 at 7:10 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi da na kansiloli a zaben kananan hukumomin Jihar Gombe da aka gudanar a ranar Asabar a kananan hukumomi 11 da kuma Sabbin Gundumomin Ci Gaba na Kananan Hukumomi (LCDAs) guda 13 na jihar.

Da yake bayyana sakamakon zaben a Gombe, Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Gombe (GOSIEC), Alhaji Garba Abdu Talasse, ya ce jam’iyyu shida ne suka shiga zaben.

Jam’iyyun sun hada da African Action Congress (AAC), All Progressives Congress (APC), Democratic Leadership Alliance (DLA), National Rescue Movement (NRM), Youth Party (YP), da Zenith Labour Party (ZLP).

Alhaji Talasse ya bayyana cewa duk da cewa jam’iyyun shida sun shiga zaben, ba dukkansu ne suka tsayar da ‘yan takara a kowace kujerar da aka fafata ba.

Ya bayyana yadda aka gudanar da zaben a matsayin mai cike da zaman lafiya, tsari da nasara.

A cewarsa, jam’iyyar APC ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi 24 da aka fafata a kananan hukumomi 11 da kuma LCDAs 13 na jihar.

Hakazalika, jam’iyyar ta samu nasarar lashe dukkan kujerun kansiloli 240 da aka fafata a fadin jihar.

Shugaban GOSIEC, Alhaji Garba Abdu Talasse, ya yaba wa al’ummar Jihar Gombe saboda yadda suka gudanar da kansu cikin lumana yayin zaben.

Ya kuma gode wa Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa samar da yanayi mai kyau da kuma goyon bayan da ya bayar wanda ya taimaka wajen gudanar da zaben cikin nasara.

Haka nan ya yaba wa dukkan jam’iyyun siyasa da masu sa ido kan zabe saboda gudummawar da suka bayar wajen tabbatar da cewa an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da nasara.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
Sarkin Musulmi Ya Ziyarci Shugaba Bola Tinubu Afrika
Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
  • Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine Amurka
  • Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru Afrika
  • Adamu: “Yakar Cin Hanci Daga Tushe Itace Mafita Daya Tilo” Labarai
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
  • Putin, Sakon Sabuwar Shekara Ya Jinjinawa Dakarun Rasha Da Suke Yaki A Ukraine Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.