Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi da na kansiloli a zaben kananan hukumomin Jihar Gombe da aka gudanar a ranar Asabar a kananan hukumomi 11 da kuma Sabbin Gundumomin Ci Gaba na Kananan Hukumomi (LCDAs) guda 13 na jihar.
Da yake bayyana sakamakon zaben a Gombe, Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Gombe (GOSIEC), Alhaji Garba Abdu Talasse, ya ce jam’iyyu shida ne suka shiga zaben.
Jam’iyyun sun hada da African Action Congress (AAC), All Progressives Congress (APC), Democratic Leadership Alliance (DLA), National Rescue Movement (NRM), Youth Party (YP), da Zenith Labour Party (ZLP).
Alhaji Talasse ya bayyana cewa duk da cewa jam’iyyun shida sun shiga zaben, ba dukkansu ne suka tsayar da ‘yan takara a kowace kujerar da aka fafata ba.
Ya bayyana yadda aka gudanar da zaben a matsayin mai cike da zaman lafiya, tsari da nasara.
A cewarsa, jam’iyyar APC ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi 24 da aka fafata a kananan hukumomi 11 da kuma LCDAs 13 na jihar.
Hakazalika, jam’iyyar ta samu nasarar lashe dukkan kujerun kansiloli 240 da aka fafata a fadin jihar.
Shugaban GOSIEC, Alhaji Garba Abdu Talasse, ya yaba wa al’ummar Jihar Gombe saboda yadda suka gudanar da kansu cikin lumana yayin zaben.
Ya kuma gode wa Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa samar da yanayi mai kyau da kuma goyon bayan da ya bayar wanda ya taimaka wajen gudanar da zaben cikin nasara.
Haka nan ya yaba wa dukkan jam’iyyun siyasa da masu sa ido kan zabe saboda gudummawar da suka bayar wajen tabbatar da cewa an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da nasara.


