Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC
Published: June 27, 2026 at 7:10 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi da na kansiloli a zaben kananan hukumomin Jihar Gombe da aka gudanar a ranar Asabar a kananan hukumomi 11 da kuma Sabbin Gundumomin Ci Gaba na Kananan Hukumomi (LCDAs) guda 13 na jihar.

Da yake bayyana sakamakon zaben a Gombe, Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Gombe (GOSIEC), Alhaji Garba Abdu Talasse, ya ce jam’iyyu shida ne suka shiga zaben.

Jam’iyyun sun hada da African Action Congress (AAC), All Progressives Congress (APC), Democratic Leadership Alliance (DLA), National Rescue Movement (NRM), Youth Party (YP), da Zenith Labour Party (ZLP).

Alhaji Talasse ya bayyana cewa duk da cewa jam’iyyun shida sun shiga zaben, ba dukkansu ne suka tsayar da ‘yan takara a kowace kujerar da aka fafata ba.

Ya bayyana yadda aka gudanar da zaben a matsayin mai cike da zaman lafiya, tsari da nasara.

A cewarsa, jam’iyyar APC ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi 24 da aka fafata a kananan hukumomi 11 da kuma LCDAs 13 na jihar.

Hakazalika, jam’iyyar ta samu nasarar lashe dukkan kujerun kansiloli 240 da aka fafata a fadin jihar.

Shugaban GOSIEC, Alhaji Garba Abdu Talasse, ya yaba wa al’ummar Jihar Gombe saboda yadda suka gudanar da kansu cikin lumana yayin zaben.

Ya kuma gode wa Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa samar da yanayi mai kyau da kuma goyon bayan da ya bayar wanda ya taimaka wajen gudanar da zaben cikin nasara.

Haka nan ya yaba wa dukkan jam’iyyun siyasa da masu sa ido kan zabe saboda gudummawar da suka bayar wajen tabbatar da cewa an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da nasara.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye
Next Post: Tinubu Na Kokarin Rage Tsadar Sufuri Ta Hanyar Shirin CNG

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jana’izar Jagoran Ƙolin Iran Ta Kawo Tsauraran Matakan Tsaro A Tehran Afrika
Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai
Malaman Tsangaya A Gombe Sun Goyi Bayan Inuwa Yahaya Da Jamilu Gwamna Afrika
NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika
An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
  • Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ Afrika
  • Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
  • Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami Najeriya
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.