Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka
Published: February 8, 2026 at 10:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin wajen Iran ya fada ranar Asabar cewa, Farisa zata kai hari kan sansanonin mayakan Amurka da suke gabas ta tsakiya, ministan wanda yayi magana ranar Asabar yace kada a dauka matakin a zaman kai hari ga kasashen da suka bada masauki ga dakarun na Amurka ba.

Ministan harkokin wajen Abbas Araqchi, wanda yayi magana da tashar talabijin ta Aljazeera, kwana daya bayan da hukumomin Iran da Washington suka ce za su ci gaba da tattaunawar da suke yi ba kai tsaye ba, game da shirin Nukiyar kasar, tattaunawar da duka bangarorin biyu suka yaba dashi a zaman da suka yi a ranar jumma’a a Oman.

Araqchi yace ba’a tsaida rana domin ci gaba da tattaunawar ba, amma shugaba Trump yace za’a yi zagaye na biyu na shawarwarin a farkon mako mai zuwa, ministan harkokin wajen yace duka sassan biyu sun amince da yin haka ba tare da bata lokaci ba.

Shugaba Trump yayi barazanar zai kai wa Iran hari bayan da Amurkan ta jibge jiragen yakin ruwa a yankin, inda ta bukaci Iran ta daina sarrafa ma’adinan Uranium, da zai bata damar kera makamin Nukiya, da kuma tsaida kera makamai masu linzami, da kuma ta daina bada goyon bayan da take yi ga kungiyoyin ‘yan tawaye a yankin.

Yayinda duka sassan biyu suka nuna a shirye suke su farfado da shawarwari kan shirin nukiliyar kasar da take rigima da kasashen yamacin duniya akai, Araqchi yaki ya amince a fadada batutuwa da shawarwarin zai taba.

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa
Next Post: Anyi Janazar ‘Yan Shi’a 33 Da Aka Kashe A Masallacin Juma’a

Karin Labarai Masu Alaka

Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran Afrika
An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Ga Watan Ramadan A Najeriya Da Nijar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari Najeriya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika
  • Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.