Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash
Published: November 17, 2025 at 11:50 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

An yanke hukumcin kisa yau Litinin a kan tsohuwar firayim ministar Bangladesh, Sheikh Hasina, da daya daga cikin manyan mukarrabanta, a saboda matakan da suka dauka na murkushe zanga-zangar dalibai da ta yi sanadin kashe daruruwan mutane a shekarar da ta shige.

Kotun da ta yi zama a Dhaka, babban birnin kasar, ta yanke hukumcin a kan Hasina da tsohon ministan harkokin cikin gidanta, Asaduz-Zaman JKhan, a saboda hannun da suke da shi wajen daukar matakin babu sani babu sabo a kan ‘yan zanga-zangar da ta kawo karshen mulkinta na shekara 15 a kasar.

An yanke wannan hukumcin ne a bayan idon Hasina da Khanm, wadanda suka gudu zuwa kasar Indiya tun bara. Ya zuwa yanzu, Indiya ta ce ba zata mika su ba, abinda ke nufin cewa zai yi wuya a aiwatar da hukumcin kisan a kansu.

Wani jami’in gwamnatin wucin gadi ta Bangladesh, yace an kashe mutane fiye da 800, aka raunata wasu fiye da dubu 14 a zanga-zangar da dalibai suka jagoranta a watannin Yuli da Agusta na shekarar da ta shige.

Labarai

Post navigation

Previous Post: An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya!
Next Post: Shin Ko Ganawar Zelensky Da Macron Zata Haifar Da ‘Da Mai Ido?

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Gombe Ta Aza Tubalin Gina Sakatariyar Gundumomin Cigaba (LCDAs) Labarai
Iran Tace Jakadan Kasar Ta A Lebanon Zai Cigaba Da Zama A Beirut Afrika
Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
  • Bayan Shafe Shekaru Hudu A Mulki Sarkin Hausawan Ibadan Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
  • Kungiyar Kiristoci Ta Karyata Kubutar Da Mambobin Su A Kaduna Afrika
  • Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.