Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin
Published: December 7, 2025 at 3:20 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Gwamnatin Jamhuriyar Benin ta ce dakarun sojojinta sun murkushe wani yunkurin juyin mulki, a bayan da wasu sojoji suka fito cikin tashar telebijin ta ƙasar suna iƙirarin kwace mulki.

Wannan yunkurin juyin mulki na baya bayan nan a yankin Afirka ta Yamma, inda sojoji suka kwace mulki a makwabtan Benin, watau Nijar da Burkina Faso, da kuma a ƙasashen Mali da Guinea-Conakry.

Ko a watan da ya shige ma, sojojin sun kwace mulki a kasar Guinea-Bissau.

Da sanyin safiyar yau lahadi, sojoji akalla 8 suka fito a gidan telebijin na kasar, wasu ɗauke da bindigogi, su na sanar da cewa wani kwamitin soja a karkashin jagorancin Kanar Tigri Pascal, ta karɓe ragamar mulkin ƙasar, tare da dakatar da yin aiki da tsarin mulki da kuma rufe bakin iyakokinta ta sama da kasa da ta ruwa.

‘Yan sa’o’i kaɗan a bayan wannan, ministan harkokin cikin gidan Benin, Alassane Seidou, ya fito a telebijin na ƙasa yana fadin cewa rundunar sojoji ta murkushe juyin mulkin.

Seidou yayi kira ga jama’a da su fito su ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum.

Wani kakakin gwamnatin Jamhuriyar Benin, yace ya zuwa yammacin nan agogon kasar, an kama mutane akalla 14 dangane da yunkurin juyin mulkin.

Afrika, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali
Next Post: ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
Shugaba Trump Yace Akwai Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Iran Afrika
An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar Najeriya
  • Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika
  • An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Iran Ta Kai Hari Matatar Mai A Kuwait Afrika
  • Kudaden Shigan Kasar Namibia Ya Bunkasa Saboda Tashin Farashin Gwal Labarai
  • Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.