Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya!
Published: November 17, 2025 at 5:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 17, 2025

A wani harin da ‘yan-bindiga suka kai a cikin daren jiya Assabar, wayewar garin yau Lahadi a wata sakandaren ‘Yan Mata dake garin Maga wato (GGCSS Maga) a karamar hukumar Danko/Wasagu a jihar Kebbi Yan Bindigar sunyi garkuwa da Dalibai Mata 25 tare da kisan Mataimakin Shugaban Makarantar.
Al’umar garin Maga da  na Makarantar yanzu haka suna cikin firgici da damuwa sakamakon faruwar Lamarin.
Mazauna yankin sun ce maharan sun farwa makarantar ne da daddare, inda suka gudanar da aika-aikar su ba tare da wata ta gargada ba, kamar yada wata mazauniyar unguwar Murjanatu Hassan Gishiri ta bayyana lamarin a matsayin wani abin takaici da ya jefa daukacin masarautar Zuru cikin alhini.
Wani magidanci da ya zanta da gidan rediyon Amurka ke Magana yace an harbe mataimakin shugaban makarantar Malam Hassan Yakubu Makuku lokacin da yake kokarin kare daliban, yayinda wani ma’aikacin Makarantar Malam Ali Shehu, ya samu raunin harbin bindiga a hannu shi.
Rumdunar ‘Yan sandan jihar Kebbi a ta bakin mai magana da yawun ta CSP Nafi’u Abubakar ya tabbatar da faruwar Lamarin tare da bayyana cewa an sace dalibai 25 a yayin samamen.
A cewar rundunar ‘yan sandan, an tura tawagar hadin gwiwa ta rundunonin ‘yan sanda, da sojoji, da ‘yan banga domin binciken hanyoyin ‘yan bindigar a dazuzzukan da ke kusa da su da nufin ceto daliban tare da kamo maharan.
Kwamishinan ‘yan sanda Bello M. Sani ya tabbatar wa mazauna yankin kudurin hukumar na kare rayuka da dukiyoyi. Ya kuma bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, su kuma lura, tare da tallafa wa ayyukan tsaro a yayin da ake ci gaba da bincike da ceto daliban.
Wasu mazauna yankin sun tabbatar da hakan a wata zanta da  suka yi da GTA Hausa, sun ce Jiragen Sojin Saman Najeriya na cigaba da shawagi a yankin, lamarin da ke nuna Dakarun Sojin sun fara aikin ceto Daliban.
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki
Next Post: An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash

Karin Labarai Masu Alaka

CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika
Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fiye Da Mutane 108 Sun Rasa Rayukansu A Ambaliyar Kenya Afrika
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
  • Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
  • Tattalin Arzikin Kasar Bahrain Ya Bunkasa Sakamakon Ruruwar Masu Yawon Bude Ido Labarai
  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
  • Muhawara Mai Zafi Tsakanin APC da ADC Shirye-Shirye
  • CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya Najeriya
  • Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.