Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki
Published: November 17, 2025 at 6:34 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Da farko a karshen makon jiya ne babbar jam’iyyar adawa a Najeriya PDP ta gudanar da taronta na kasa a birnin Badun, babban birnin jihar Oyo. inda ta zabi sabbbin shugabanni. Lauya Kabiru Tanimu Turaki, shine aka zaba sabon shugaban jam’iyyar. Aka kuma zabi Taofeek Arapaja, a matsayin sakataren jam’iyya. Babban taron ya kuma kori wasu jiga-jigan jam’iyyar da suka hada da Ministan raya birnin Tarayya Abuja Nyesom Wike da wadansu, kan zargin suna yiwa jam’iyyar zagon kasa.

Don samun haske akan wannan dambarwar, abokin aikin mu Yusuf Aliyu Harande ya tattauna da wani masanin siyasa kuma lauya mai zaman kanshi.

“Akwai bukatar jam’iyyu a Najeriya su dinga mutunta hukunce-hukuncen Kotuna, ba don komai ba kuwa sai don mutunta doka da oda daga mahukunta. Rashin mutunta hukuncin kotu da jam’iyar PDP ta yi zai iya jefa ta cikin mawuyacin hali.” A cewar Lauya Bala Usman, wani lauya mai zaman kanshi a Abuja.

Sau da yawa idan kaga ana takaddama, to abu da yafi kamata shine a garzaya kotu, don magance matsalar, kamar yadda Alh. Sule Lamido, tsohon gwamnan jihar Jigawa, yayi na garzayawa kotu bayan hana shi sayen form da aka yi na tsayawa takarar shugabancin jam’iyar. Wani abu ne da zai iya haifar da babbar matsala a cikin jami’iyar a gaba.

Duk kuwa da cewar kotu ta bada umurnin kada a yi wannan taron, baya ga karar da Lamido ya shigar, wata kotu ta bada akasasin wannan hukunci, shi yasa wasu ‘yan jam’iyyar cigaba da gabatar da taron.

Barista Bala, yana kira da mahukunta da su dinga mutunta hukuncin kotu, da kuma yin amfani da matsayin su na siyasa don yin garon bawul ga bangaren shari’ar kasar, don gujewa irin wadannan matsalokin.

Yana kuma ganin wannan taron bashi da hurumin zaben wannan shugaban da suke ikirarin sun yi da kuma korar wasu ‘yan jam’iyar. Lallai babu shakka idan aka koma wajen wannan kotun zata soke wannan taron, da cire sabon shugaban jam’iyyar da aka zaba.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/Rikicin-Jamiyyar-PDP.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau
Next Post: An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya!

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika
Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Sanatan Nasarawa Ta Arewa Ya Rasu A Kasar India Najeriya
Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland Amurka
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
  • Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
  • Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto Tsaro
  • Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.