Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki
Published: November 17, 2025 at 6:34 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Da farko a karshen makon jiya ne babbar jam’iyyar adawa a Najeriya PDP ta gudanar da taronta na kasa a birnin Badun, babban birnin jihar Oyo. inda ta zabi sabbbin shugabanni. Lauya Kabiru Tanimu Turaki, shine aka zaba sabon shugaban jam’iyyar. Aka kuma zabi Taofeek Arapaja, a matsayin sakataren jam’iyya. Babban taron ya kuma kori wasu jiga-jigan jam’iyyar da suka hada da Ministan raya birnin Tarayya Abuja Nyesom Wike da wadansu, kan zargin suna yiwa jam’iyyar zagon kasa.

Don samun haske akan wannan dambarwar, abokin aikin mu Yusuf Aliyu Harande ya tattauna da wani masanin siyasa kuma lauya mai zaman kanshi.

“Akwai bukatar jam’iyyu a Najeriya su dinga mutunta hukunce-hukuncen Kotuna, ba don komai ba kuwa sai don mutunta doka da oda daga mahukunta. Rashin mutunta hukuncin kotu da jam’iyar PDP ta yi zai iya jefa ta cikin mawuyacin hali.” A cewar Lauya Bala Usman, wani lauya mai zaman kanshi a Abuja.

Sau da yawa idan kaga ana takaddama, to abu da yafi kamata shine a garzaya kotu, don magance matsalar, kamar yadda Alh. Sule Lamido, tsohon gwamnan jihar Jigawa, yayi na garzayawa kotu bayan hana shi sayen form da aka yi na tsayawa takarar shugabancin jam’iyar. Wani abu ne da zai iya haifar da babbar matsala a cikin jami’iyar a gaba.

Duk kuwa da cewar kotu ta bada umurnin kada a yi wannan taron, baya ga karar da Lamido ya shigar, wata kotu ta bada akasasin wannan hukunci, shi yasa wasu ‘yan jam’iyyar cigaba da gabatar da taron.

Barista Bala, yana kira da mahukunta da su dinga mutunta hukuncin kotu, da kuma yin amfani da matsayin su na siyasa don yin garon bawul ga bangaren shari’ar kasar, don gujewa irin wadannan matsalokin.

Yana kuma ganin wannan taron bashi da hurumin zaben wannan shugaban da suke ikirarin sun yi da kuma korar wasu ‘yan jam’iyar. Lallai babu shakka idan aka koma wajen wannan kotun zata soke wannan taron, da cire sabon shugaban jam’iyyar da aka zaba.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/Rikicin-Jamiyyar-PDP.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau
Next Post: An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya!

Karin Labarai Masu Alaka

An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya Najeriya
Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
  • Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
  • Hukumar IMF Tana Naziri Domin Kara Bada Lamuni Ga Kasar Zambiya Afrika
  • Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
  • An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.