Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki
Published: November 17, 2025 at 6:34 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Da farko a karshen makon jiya ne babbar jam’iyyar adawa a Najeriya PDP ta gudanar da taronta na kasa a birnin Badun, babban birnin jihar Oyo. inda ta zabi sabbbin shugabanni. Lauya Kabiru Tanimu Turaki, shine aka zaba sabon shugaban jam’iyyar. Aka kuma zabi Taofeek Arapaja, a matsayin sakataren jam’iyya. Babban taron ya kuma kori wasu jiga-jigan jam’iyyar da suka hada da Ministan raya birnin Tarayya Abuja Nyesom Wike da wadansu, kan zargin suna yiwa jam’iyyar zagon kasa.

Don samun haske akan wannan dambarwar, abokin aikin mu Yusuf Aliyu Harande ya tattauna da wani masanin siyasa kuma lauya mai zaman kanshi.

“Akwai bukatar jam’iyyu a Najeriya su dinga mutunta hukunce-hukuncen Kotuna, ba don komai ba kuwa sai don mutunta doka da oda daga mahukunta. Rashin mutunta hukuncin kotu da jam’iyar PDP ta yi zai iya jefa ta cikin mawuyacin hali.” A cewar Lauya Bala Usman, wani lauya mai zaman kanshi a Abuja.

Sau da yawa idan kaga ana takaddama, to abu da yafi kamata shine a garzaya kotu, don magance matsalar, kamar yadda Alh. Sule Lamido, tsohon gwamnan jihar Jigawa, yayi na garzayawa kotu bayan hana shi sayen form da aka yi na tsayawa takarar shugabancin jam’iyar. Wani abu ne da zai iya haifar da babbar matsala a cikin jami’iyar a gaba.

Duk kuwa da cewar kotu ta bada umurnin kada a yi wannan taron, baya ga karar da Lamido ya shigar, wata kotu ta bada akasasin wannan hukunci, shi yasa wasu ‘yan jam’iyyar cigaba da gabatar da taron.

Barista Bala, yana kira da mahukunta da su dinga mutunta hukuncin kotu, da kuma yin amfani da matsayin su na siyasa don yin garon bawul ga bangaren shari’ar kasar, don gujewa irin wadannan matsalokin.

Yana kuma ganin wannan taron bashi da hurumin zaben wannan shugaban da suke ikirarin sun yi da kuma korar wasu ‘yan jam’iyar. Lallai babu shakka idan aka koma wajen wannan kotun zata soke wannan taron, da cire sabon shugaban jam’iyyar da aka zaba.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/Rikicin-Jamiyyar-PDP.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau
Next Post: An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya!

Karin Labarai Masu Alaka

Bayan Shekaru Biyar, Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Gano Motar da Aka Sace A Fatakwal Afrika
Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba Najeriya
Fadar Shugaban Kasa Ta Karyata Jita-Jitar Yunkurin Sanya Wa Tinubu Guba A Abinci Afrika
Allah Ya Yiwa Shahararren Dan Jarida Saleh Shehu Ashaka Rasuwa Labarai
Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • ‘Yan Sanda A Jihar Gombe Sun Karyata Kona Gidan Nafiu Bala Afrika
  • An Karrama Darakta Janar Na DSS Bisa Ƙoƙarinsa Na Inganta Alaƙar Hukumomin Tsaro Da Kafafen Yaɗa Labarai Afrika
  • Kungiyar Tsaro Ta NATO Tana Fuskantar Kalubale Afrika
  • Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
  • AIG Kwaimo Ya Kai Ziyarar Aiki Gombe, Ya Buƙaci Ƙara Ƙaimi A Yaƙi Da Ta’addanci Labarai
  • Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.