Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato
Published: March 16, 2026 at 8:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Al’ummar kauyen Wanka dake karamar hukumar Kanam a Jihar Filato sun nemi hukumomi su kai musu dauki, bayan watsewarsu daga kauyen, biyo bayan kisan sojoji da ‘yan banga da ‘yan ta’adda suka yi a karshen makon jiya.

Garin Wanka, wanda ke yankin Garga a karamar hukumar Kanam a jihar Filato, na makwabtaka da karamar hukumar Alkalerin jihar Bauchi kusa da dajin da ‘yan bindiga ke cin karensu babu babbaka.

Wani mazaunin garin na Wanka da ya bukaci in sakaya sunanshi saboda tsaro, yace ‘yan bindigar sun kashe sojoji goma sha hudu da ‘yan banga biyar, lamari kenan da ya sanya suka watse daga kauyen.

Duk da cewa kafafen yada labarai sun yayata batun kisan sojojin, rundunar dake wanzadda zaman lafiya a yankin, Operation Enduring Peace bata fitar da sanarwa kan batun ba.

Bayanai sun nuna cewa sojojin da aka kashen suna aikin tabbatar da tsaro ne a yankin, kafin ‘yan bindigar su yi musu kwanton bauna suka hallaka su.

Haka ma bayanan da ba’a tantance ba sun nuna cewa sojoji sun hallaka ‘yan ta’adda fiye da ishirin a yankin na Wanka.

A wata sanarwa da gwamnatin jihar Filato ta fitar da sanya hannun komishinan yada labarai da sadarwa, Madam Joyce Ramnap tace gwamnati na kan bakanta na tsaron lafiyar jama’a da dukiyoyinsu.

Sanarwar tace gwamnati ta hada gwiwa da jami’an tsaro don kara azama wajen tabbatar da tsaro a dukkan yankunan dake fuskantar barazanar tsaro a fadin jihar.

Mai fashin baķi kan lamura kuma sakataren kungiyar dake raya al’ummar Kanam, Nuhu Shehu Kanam yace matsalar tsaro a yankin ba sabon abu bane amma hukumomi sun kasa shawo kanta.

Bayanai na nuni da cewa ayyukan masu bada bayanai wa ‘yan ta’adda, da aka fi sani da informants, suna tasiri wajen samun cikkas da yaki da matsalolin tsaro a yankin na Garga da kewaye.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260316-WA0040.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sarkin Musulmi Ya Ziyarci Shugaba Bola Tinubu
Next Post: Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Sakamakon Rikicin Gabas Ta Tsakiya Farashin Mai Ya Karu Labarai
Paparoma Leo: Zai Kai Ziyara Ƙasar Angola Labarai
An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda Siyasa
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar Siyasa
  • Ukraine Takai Hari Wajen Kera Makami Mai Linzami A Rasha Labarai
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
  • Gombe Ta Ƙaddamar da Allurar Rigakafin HIV Ta LEN PrEP Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.