Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo
Published: November 25, 2025 at 2:12 PM | By: Bala Hassan | Updated: November 25, 2025

Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist

Tabbas Wikki Tourist ta samu shuwagabanin da zasu cire mata kitse a wuta. Wannan yabo ya fito ne ta bakin Shugaban ƙungiyar Magoya bayan Ƙungiyar kwallon kafa ta Wikki Tourist Fc da ke Bauchi a tarayyar Najeriya. Alh Umar (Aljan) yayi karin hasake a wata ganawa da yayi da wakilin GTA Hausa.

Umar ya ce ƙungiyar ta samu dai dai tuwa a karkashin jagorancin shugaban gudanawar Kulub din Alh. Auwal Gotel, lura da yadda ƙungiyar ta ke samun nasara a wasannin ta a gida da waje ” In ji Aljan.

Yace a baya akwai wasu abubuwa na kurakurai da aka yi bangaren Shuwagabanni sakamakon jan hankali da ake musu ta kafafen yada labari ko mai ya dai dai ta a yanzu.

Har ila yau ‘Aljan, ya yaba wa manbobinsa bangaren magoya baya bisa yadda suke bin doka da oda wajan ganin anyi wasa lafiya, don kuwa ko da za’a zo gida a Wikki Tourist ta yi kunnen doki baza a ta da yamutsi ba, kamar yadda wasu ƙungiyoyin ke yi.

A ranar Lahadi da ta gabata ƙungiyar kwallon kafa ta Bayelsa United ta zo har gida ta rike Wikki 1-1 a wasan mako na 14, cikin gasar Firimiyar Najeriya na bana, amman babu wani abun da ya faru na cin mutuncin alkalin wasa ko wani jami’i, duk da irin kurakuren da baza’a rasa ba daga Alkalin wasa.

Umar yace duk kulub din Arewa da suke buga gasar Firimiyar Najeriya NPFL 2025/26 babu wadda ta kai Wikki Tourist kokari ganin yadda ita ce kawai ba’ayi nasara akanta a gidan ta ba.

Yanzu haka Wikki Tourist FC ta na mataki na 7 a teburen gasar Firimiyar Najeriya mako na 14, a ranar Asabar 29 ga watan Nuwamban 2025, zata kai bakunci zuwa gidan ƙungiyar kwallon kafa ta Bendel Insurance FC, wasannin mako na 15.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City
Next Post: An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi

Karin Labarai Masu Alaka

Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka Wasanni
Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan Labarai
  • Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
  • Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
  • Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako Afrika
  • An Katse Intanet Da Wayar Tarho A Kasar Uganda Siyasa
  • An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
  • Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
  • An Gudanar Da Tiyatar Ido Kyauta A Gombe Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.