Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya
Published: January 11, 2026 at 10:06 PM | By: Bala Hassan | Updated: January 11, 2026

CAF Ta fara Bincike Kan Rikicin Bayan tashi a Wasan Algeria Da Najeriya.

Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF) ta fara bincike a hukumance kan munanan abubuwan da suka biyo bayan wasan kwata-final na Kofin Kasashen Afirka tsakanin Algeria da Najeriya a daren Asabar,

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, CAF ta tabbatar da cewa ‘yan wasan Algeria da membobin ma’aikatan bangaren masu horaswa sun tunkari alkalin wasan jim kadan bayan an busa tashi a wasan.

An ruwaito cewa lamarin ya kara kamari yayin da wasu daga cikin ‘yan wasan Algeria suka bi alkalan wasa zuwa cikin hanyar tafiyarsa zuwa dakin hutawa da aka tanadar masa, wani abu da CAF ta kira “abin da ba za a yarda da shi ba” kuma ya saba wa dokokin ladabtarwa na gasar.

CAF ta kuma bayyana cewa tana duba rahotannin rikicin da ya shafi ‘yan jarida da sauran ma’aikatan kafofin watsa labarai bayan tashi a wasan, yayin da tashin hankali ya bazu a wajen filin wasa.

Wasan Algeria da Najeriya, wanda aka buga a Marrakech, ya ƙare da 2-0 nasara ga Super Eagles, ta Najeriya sakamakon da ya haifar da yanayin hayaniya daga sansanin Algeria.

Hukumar ta tabbatar da cewa za a yi nazari sosai kan dukkan rahotannin wasanni, na gabatar da alkalan wasa, da kuma shaidun bidiyo a matsayin wani bangare na binciken.

CAF ta kara da cewa za a sanar da matakan ladabtarwa da suka dace da zarar an kammala binciken.

Wannan lamari na ci gaba da kara haifar da cece-kuce a wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin zakarun Afirka, yayin da AFCON 2025 ke shirin shiga mataki mai muhimmanci na wasan dab da karshen.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa
Next Post: Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku

Karin Labarai Masu Alaka

Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
  • Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
  • Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
  • Kasuwannin Hannun Jari Sun Farfado Afrika
  • Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
  • Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.