Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu
Published: December 19, 2025 at 2:56 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Al’ummar Arewa a Jihar Inugu na ci gaba da yin sam-barka tare da bayyana farin ciki da bude sabon gidan damben gargajiya da aka yi a Inugu babban birnin jihar bayan shafe shekaru da wasan ya dauke.

Mai gidan damben Cif Emeka Nnolim, wani dan kabilar Igbo ya ce, “Wannan hanya ce ta hada kawunan kabilu daban-daban na Najeriya don karfafa zumunci ta hanyar raya wasan dambe a tsakanin matasan Arewa da ke wannan jihar da wadanda suke nesa. Wannan matakin farko ne na bunkasa wasannin gargajiya a Jihar Inugu don mayar da jihar cibiyar wasannin gargajiya a Najeriya.”

Bayan kammala bude filin wasan, shugaban al’ummar Arewa a jihar da kuma babban mai taimaka wa gwamnan Jihar Inugu kan ayyuka na musamman, Alhaji Abubakar Yusuf Sambo ya tofa albarkacin bakinsa kan dawowar wasan dambe a jihar.

“Na yi farin ciki da ganin cewa da duk da cewa muna kudancin Najeriya muna tuna abin da aka san Arewa da shi watau wasan dambe. Wasa ne na hada zumunci, kuma duk inda ake irin wannan zamu bada goyon baya,” inji Alhaji Yusuf Sambo.

A cewar wani dan dambe dan asalin garin Hadejia na Jihar Jigawa mai suna Adamu wanda aka fi sani da Shagon Baturiya, “Wasa ya yi dadi yadda ake so. Sabon gidan dambe da aka bude anan Inugu ya yi kyau. Na yi farin ciki kuwa,” a yayin da wani shahararren dan wasa Badaman Bauchi, shi ma cike da farin ciki, ya mika goron gayyata zuwa daukacin ‘yan wasa da cewa:

“Filin sabon gidan wasan dambe da aka bude a Inugu ba laifi. Toh domin haka, muna kira ga sauran ‘yan wasa da suke nesa da su zo. Muna gayyatar kowa da kowa su zo.”

An bude gidan damben ne unguwar Emene wacce take cikin birnin Inugun, inda matasan Arewa sun fara tururuwa don nishadantar da kansu da take taken ‘yan wasa da kide-kiden gargajiya masu faranta ran gaske.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025. Wasanni
Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Masar Ta Kayyade Farashin Buradi A Kasar Afrika
  • Shirin Dare 26.11.2025 Rediyo
  • Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
  • An Zargi Kasar Eritrea Da Cin Zarafin Sojojin Habasha Afrika
  • Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
  • Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.