Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali
Published: December 23, 2025 at 5:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugabanin kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso sun fara gudanar da taron kolin kungiyar AES a wannan litinin 22 ga watan disamban 2025 da nufin tattauna batutuwa da dama da suka shafi yankin da rayuwar al’umomin kasashen 3 masu fama da matsaloli iri daya musamman aika aikar kungiyoyin ta’addanci. wasu ‘yan Nijar suka fara bayyana fatansu kan wannan taro kamar yadda za a ji a wannan rahoto da wakilin GTA Hausa Amurka ke Magana Souley Moumouni Barma ya aiko mana daga Yamai.

Janar Abdourahamane Tiani na Nijar da Keftin Ibrahim Traore na Burkina Faso da Assimi Goita na Mali shugaban rikon kungiyar AES a yayin zaman na wuni biyu za su yi bitar ayyukan hadin guiwar da suka gudanar a kungiyance kafin su tattauna kan batutuwan da zasu fi baiwa fifiko a nan gaba musamman ta inda za su bullowa lamarin tsaro, tattalin arziki aiyukan ci gaban jama’a diflomasiya da dai sauransu. shin ko ya ‘yan Nijar ke kallon wannan taro.?

Koda yake yanayin tsaro na kan gaban abubuwan da aka fi nuna damuwa kansu, ‘yan fafutika irinsu Hamidou Sidi Fody na kungiyar kulawa da Rayuwa na shawartar shugabanin kasashen 3 su kuma kara duba wata matsalar ta daban da ke dabaibaye harakokin tattalin arziki.

Nijar da Mali da Burkina Faso na cikin wata fafutikar tabbatar da ‘yancin kai a yayin da alamu ke nuna bayyanar babban sauyi a tafiyar siyasar duniya ta yau. abin da ke kara wa jama’ar yankin AES kwarin guiwa a game da manufofin da shugabanin kasashen 3 suka sa gaba sai dai akwai abin lura.

kungiyar AES ta samo asali a watan satumban 2023 kafin ta zama gamayya bayan watanni biyu da zumma duba alkibla guda a game da dukkan batutuwan da suka shafi tsaro diflomasiya tattalin arziki da sauransu, kasashen 3 sun fice daga CEDEAO a janerun 2024 saboda zargin kungiyar da zama ‘yar amshin shatan kasashen yammaci. sannan sun kori sojojin Faransa daga yankin sahel. daga bisani sun kafa rundunar hadin guiwa mai dakaru 5000 wace a karshen makon jiya aka kaddamar da aiyukanta a hukumance a ci gaba da jan damarar yaki da kungiyoyin ta’addanci.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi
Next Post: Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje Afrika
Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Kudurin Kasar Ghana Afrika
Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
Jami’an Shiga Da Fice A Afirka Ta Kudu Sun Tafka Badakalar Kudade Afrika
Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya Afrika
Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
  • CHAN Ta Duba Lafiyar Idanun ‘Yan Jarida A Filato Afrika
  • Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
  • Lakurawa Sun Kashe A Ƙalla A Mutane 34 A Jihar Kebbi Labarai
  • Ba Mamaki APC Ta Kafa Tarihi A Ranar Litinin Najeriya
  • Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.