Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali
Published: December 23, 2025 at 5:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugabanin kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso sun fara gudanar da taron kolin kungiyar AES a wannan litinin 22 ga watan disamban 2025 da nufin tattauna batutuwa da dama da suka shafi yankin da rayuwar al’umomin kasashen 3 masu fama da matsaloli iri daya musamman aika aikar kungiyoyin ta’addanci. wasu ‘yan Nijar suka fara bayyana fatansu kan wannan taro kamar yadda za a ji a wannan rahoto da wakilin GTA Hausa Amurka ke Magana Souley Moumouni Barma ya aiko mana daga Yamai.

Janar Abdourahamane Tiani na Nijar da Keftin Ibrahim Traore na Burkina Faso da Assimi Goita na Mali shugaban rikon kungiyar AES a yayin zaman na wuni biyu za su yi bitar ayyukan hadin guiwar da suka gudanar a kungiyance kafin su tattauna kan batutuwan da zasu fi baiwa fifiko a nan gaba musamman ta inda za su bullowa lamarin tsaro, tattalin arziki aiyukan ci gaban jama’a diflomasiya da dai sauransu. shin ko ya ‘yan Nijar ke kallon wannan taro.?

Koda yake yanayin tsaro na kan gaban abubuwan da aka fi nuna damuwa kansu, ‘yan fafutika irinsu Hamidou Sidi Fody na kungiyar kulawa da Rayuwa na shawartar shugabanin kasashen 3 su kuma kara duba wata matsalar ta daban da ke dabaibaye harakokin tattalin arziki.

Nijar da Mali da Burkina Faso na cikin wata fafutikar tabbatar da ‘yancin kai a yayin da alamu ke nuna bayyanar babban sauyi a tafiyar siyasar duniya ta yau. abin da ke kara wa jama’ar yankin AES kwarin guiwa a game da manufofin da shugabanin kasashen 3 suka sa gaba sai dai akwai abin lura.

kungiyar AES ta samo asali a watan satumban 2023 kafin ta zama gamayya bayan watanni biyu da zumma duba alkibla guda a game da dukkan batutuwan da suka shafi tsaro diflomasiya tattalin arziki da sauransu, kasashen 3 sun fice daga CEDEAO a janerun 2024 saboda zargin kungiyar da zama ‘yar amshin shatan kasashen yammaci. sannan sun kori sojojin Faransa daga yankin sahel. daga bisani sun kafa rundunar hadin guiwa mai dakaru 5000 wace a karshen makon jiya aka kaddamar da aiyukanta a hukumance a ci gaba da jan damarar yaki da kungiyoyin ta’addanci.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi
Next Post: Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango

Karin Labarai Masu Alaka

Gombe Ta Yi Gasar Makarantun Firamare Don Bikin Cika Shekaru 100 Na Hassan Central Afrika
Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika
Majami’ar Anglican Zasuyi Taron Zaben Sabon Shugaba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
  • Wani Alkali A Kotun Amurka Ya Dakatar Da Kudurin Shugaba Trump Afrika
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
  • Farashin Danyen Mai Ya Farfado Fiye Da Kashi Daya Sauran Duniya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.