Jam’iyyar (PDP) reshen jihar Gombe ta yi kira ga Gwamnatin jihar Gombe da ta dakatar da aikin gina sabon ginin Majalisar Dokokin jihar, bayan rushewar wani ɓangare na simintin bene da ya yi sanadin mutuwar wasu ma’aikata tare da jikkata wasu da dama.
A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na jam’iyyar, Abdulkadir Ahmad Dukku, ya sanya wa hannu, PDP ta bayyana matuƙar alhini kan lamarin da ya faru a ranar 10 ga Yuli, 2026, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu da addu’ar samun sauƙi cikin gaggawa ga waɗanda suka jikkata.

Jam’iyyar ta buƙaci gwamnatin jihar ta tabbatar da cewa duk waɗanda suka ji rauni sun samu cikakkiyar kulawar lafiya, tallafin kuɗi da kuma diyya inda ya dace.
PDP ta kuma nemi a dakatar da duk wani aiki a wurin ginin har sai an gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa domin gano musabbabin rushewar ginin.
Sanarwar ta ce lamarin ya tayar da tambayoyi kan ko an bi ƙa’idojin aikin injiniya, tsarin kula da inganci da matakan tsaro yayin gudanar da aikin.
Jam’iyyar ta buƙaci hukumomin da abin ya shafa da ƙungiyoyin ƙwararrun injiniyoyi su gudanar da bincike cikin gaskiya da adalci domin gano ko an samu sakaci wajen tsara aikin, bayar da kwangilar, ko aiwatar da ita.
PDP ta kuma yi zargin cewa akwai yiwuwar sakaci a aikin, saboda haka ta nemi a binciki ɗan kwangilar da sauran masu ruwa da tsaki. Ta ce duk wanda bincike ya tabbatar da laifi, ko ɗan kwangila ne, mai ba da shawara ko jami’in gwamnati, ya kamata a hukunta shi bisa tanadin doka.
Jam’iyyar ta jaddada cewa rayuka da lafiyar ma’aikatan gini ba abin wasa ba ne, tana mai kira ga gwamnatin jihar da ta ɗauki matakan da za su tabbatar da adalci ga waɗanda abin ya shafa tare da hana sake faruwar irin wannan hatsari a nan gaba.


