Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

PDP Ta Nemi Bincike Kan Rushewar Ginin Majalisar Dokokin Gombe, Tayi Zargi Game Da Sakaci
Published: July 11, 2026 at 7:30 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar (PDP) reshen jihar Gombe ta yi kira ga Gwamnatin jihar Gombe da ta dakatar da aikin gina sabon ginin Majalisar Dokokin jihar, bayan rushewar wani ɓangare na simintin bene da ya yi sanadin mutuwar wasu ma’aikata tare da jikkata wasu da dama.

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na jam’iyyar, Abdulkadir Ahmad Dukku, ya sanya wa hannu, PDP ta bayyana matuƙar alhini kan lamarin da ya faru a ranar 10 ga Yuli, 2026, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu da addu’ar samun sauƙi cikin gaggawa ga waɗanda suka jikkata.

Jam’iyyar ta buƙaci gwamnatin jihar ta tabbatar da cewa duk waɗanda suka ji rauni sun samu cikakkiyar kulawar lafiya, tallafin kuɗi da kuma diyya inda ya dace.

PDP ta kuma nemi a dakatar da duk wani aiki a wurin ginin har sai an gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa domin gano musabbabin rushewar ginin.

Sanarwar ta ce lamarin ya tayar da tambayoyi kan ko an bi ƙa’idojin aikin injiniya, tsarin kula da inganci da matakan tsaro yayin gudanar da aikin.

Jam’iyyar ta buƙaci hukumomin da abin ya shafa da ƙungiyoyin ƙwararrun injiniyoyi su gudanar da bincike cikin gaskiya da adalci domin gano ko an samu sakaci wajen tsara aikin, bayar da kwangilar, ko aiwatar da ita.

PDP ta kuma yi zargin cewa akwai yiwuwar sakaci a aikin, saboda haka ta nemi a binciki ɗan kwangilar da sauran masu ruwa da tsaki. Ta ce duk wanda bincike ya tabbatar da laifi, ko ɗan kwangila ne, mai ba da shawara ko jami’in gwamnati, ya kamata a hukunta shi bisa tanadin doka.

Jam’iyyar ta jaddada cewa rayuka da lafiyar ma’aikatan gini ba abin wasa ba ne, tana mai kira ga gwamnatin jihar da ta ɗauki matakan da za su tabbatar da adalci ga waɗanda abin ya shafa tare da hana sake faruwar irin wannan hatsari a nan gaba.

Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
Next Post: Zulum Ya Tallafa Wa Mambobin NYSC Da Naira Miliyan 8.2 A Borno

Karin Labarai Masu Alaka

NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC Siyasa
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar Siyasa
  • Gaza Ga Albarusai Ga Yunwa Tsaro
  • Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
  • Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
  • Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya
  • Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta Amurka
  • Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
  • Kotun Amurka Ta Soke Harajin Fito Da Shugaba Trump Ya Kakabawa Kayan Kasashen Waje Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.