Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Zulum Ya Tallafa Wa Mambobin NYSC Da Naira Miliyan 8.2 A Borno
Published: July 12, 2026 at 2:09 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya rabawa mambobin masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) da ke aiki a ƙananan hukumomin Bayo da Hawul tallafin kuɗi da ya kai jimillar naira miliyan 8 da dubu 200 (N8.2m), a wani mataki na ƙarfafa musu gwiwa.

A ƙaramar hukumar Bayo, Gwamna Zulum ya bai wa kowane ɗaya daga cikin mambobin NYSC 29 kuɗi naira dubu hamsin (N50,000). Haka kuma, ya bai wa Corps Liaison Officer (CLO) da Local Government Inspector (LGI) naira dubu ɗari (N100,000) kowannensu. Jimillar kuɗin da aka rabawa a ƙaramar hukumar ta Bayo ta kai naira miliyan 1 da dubu 650 (N1.65m).

A ƙaramar hukumar Hawul kuwa, Gwamnan ya bai wa kowane ɗaya daga cikin mambobin NYSC 125 naira dubu hamsin (N50,000), yayin da Corps Liaison Officer (CLO) ya karɓi naira dubu ɗari (N100,000), sannan Local Government Inspector (LGI) ya karɓi naira dubu ɗari biyu (N200,000). Jimillar kuɗin da aka raba a Hawul ta kai naira miliyan 6 da dubu 550 (N6.55m).

Gaba ɗaya, ƙananan hukumomin Bayo da Hawul sun amfana da tallafin da ya kai naira miliyan 8 da dubu 200 (N8.2m).
Da yake tsokaci kan wannan tallafi, Kodinetan Hukumar NYSC na jihar Borno, Malam Nasir Bello, ya bayyana jin daɗinsa, yana mai cewa wannan karamci bai zo masa da mamaki ba, domin ya zama al’adar Gwamna Zulum na kula da jin daɗin mambobin NYSC.

Ya ƙara da cewa, ci gaba da ba da muhimmanci ga walwala da jin daɗin mambobin NYSC a jihar Borno zai ƙara jawo hankalin matasa masu yi wa ƙasa hidima su karɓi aiki a jihar cikin kwarin gwiwa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: PDP Ta Nemi Bincike Kan Rushewar Ginin Majalisar Dokokin Gombe, Tayi Zargi Game Da Sakaci
Next Post: An Yaba Wa Gwamnatin Bauchi Bisa Karban Bakuncin Gasar Polo

Karin Labarai Masu Alaka

Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani Labarai
Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta Amurka
Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wani Alkali A Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Kasar Afrika
‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai Labarai
  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
  • Sojin Saman Najeriya Sunyi Gagarumar Nasara A Yankin Borno Najeriya
  • An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai
  • CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
  • Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya Labarai
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.