Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Zulum Ya Tallafa Wa Mambobin NYSC Da Naira Miliyan 8.2 A Borno
Published: July 12, 2026 at 2:09 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya rabawa mambobin masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) da ke aiki a ƙananan hukumomin Bayo da Hawul tallafin kuɗi da ya kai jimillar naira miliyan 8 da dubu 200 (N8.2m), a wani mataki na ƙarfafa musu gwiwa.

A ƙaramar hukumar Bayo, Gwamna Zulum ya bai wa kowane ɗaya daga cikin mambobin NYSC 29 kuɗi naira dubu hamsin (N50,000). Haka kuma, ya bai wa Corps Liaison Officer (CLO) da Local Government Inspector (LGI) naira dubu ɗari (N100,000) kowannensu. Jimillar kuɗin da aka rabawa a ƙaramar hukumar ta Bayo ta kai naira miliyan 1 da dubu 650 (N1.65m).

A ƙaramar hukumar Hawul kuwa, Gwamnan ya bai wa kowane ɗaya daga cikin mambobin NYSC 125 naira dubu hamsin (N50,000), yayin da Corps Liaison Officer (CLO) ya karɓi naira dubu ɗari (N100,000), sannan Local Government Inspector (LGI) ya karɓi naira dubu ɗari biyu (N200,000). Jimillar kuɗin da aka raba a Hawul ta kai naira miliyan 6 da dubu 550 (N6.55m).

Gaba ɗaya, ƙananan hukumomin Bayo da Hawul sun amfana da tallafin da ya kai naira miliyan 8 da dubu 200 (N8.2m).
Da yake tsokaci kan wannan tallafi, Kodinetan Hukumar NYSC na jihar Borno, Malam Nasir Bello, ya bayyana jin daɗinsa, yana mai cewa wannan karamci bai zo masa da mamaki ba, domin ya zama al’adar Gwamna Zulum na kula da jin daɗin mambobin NYSC.

Ya ƙara da cewa, ci gaba da ba da muhimmanci ga walwala da jin daɗin mambobin NYSC a jihar Borno zai ƙara jawo hankalin matasa masu yi wa ƙasa hidima su karɓi aiki a jihar cikin kwarin gwiwa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: PDP Ta Nemi Bincike Kan Rushewar Ginin Majalisar Dokokin Gombe, Tayi Zargi Game Da Sakaci
Next Post: An Yaba Wa Gwamnatin Bauchi Bisa Karban Bakuncin Gasar Polo

Karin Labarai Masu Alaka

Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza Labarai
Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato Bidiyo
NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika
Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika
  • Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.